ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Sin

Ga duk mai bibiyar ci gaban da kasar Sin ta samu musamman a gwamman shekarun da suka gabata, tilas ya amince cewa salon da kasar ke bi wajen zamanantar da kai ya ciri tuta, duba da yadda ya haifarwa ’yan kasar da mai ido ta fuskar tsame alumma daga kangin talauci, da samarwa alummar Sinawa damar more ababen more rayuwa masu inganci, da raya fasahohin zamani da sauransu, wadanda dukkanin su ke zama muhimmin misali mai kima ga sauran kasashe masu tasowa musamman na Afirka.

 

Kasashen Afirka na iya koyi da dabarun kasar Sin ta fuskar aiwatar da managartan manufofin raya kai, da gudanar da sauye-sauye da zamanantarwa, ta yadda su ma za su daga matsayin su daga kasashen da alummun suke fama da karancin karfin tattalin arziki zuwa cibiyoyin raya tattalin arziki a matakin kasa da kasa.

ADVERTISEMENT
  • Xi Ya Mika Gaisuwar Ban Girma Ga Dattawa A Jajibirin Ranar Tsofaffin Kasar Sin
  • Ban Yi Nadamar Yakar PDP A Zaben 2023 Ba – Wike

Mun dai ga misalan hakan a bangaren kasar Sin, wadda ta kawar da fatara, da cike gibi tsakanin mawadata da masu rauni, zuwa wanzar da ci gaba mai dorewa a dukkanin fannoni, matakan da suka kai kasar zuwa turbar samun ci gaba a dukkanin bangarori, da daidaita tafiya tsakanin raya tattalin arzikin kasa da ci gaban zamantakewa da walwalar alumma.

 

LABARAI MASU NASABA

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

A daya hannun, muna iya cewa yadda kasashen Afirka ke kara rungumar tafiyar samar da ci gaba tare da kasar Sin, karkashin tsare-tsare, da dandaloli daban daban abun a yaba ne. A duk inda muka duba muna iya ganin ayyukan hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka na raba ababen more rayuwa, da musayar kwarewa, da musayar aladu, da karfafa kawance, da bunkasa cinikayyar hajoji da hidimomi tsakanin sassan biyu.

 

Baya ga hakan, wasu karin sassa da ya kamata sassan biyu su inganta hadin gwiwa su ne batun samar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, da kare muhallin halittu, da rage tasirin dumamar yanayi, da raya samar da makamashi mai tsafta, fannonin da tuni kasar Sin ta yi nisa a fannin cimma nasarar su.

 

Yayin da ake duba yiwuwar fadada kawance, da cudanya tsakanin Sin da kasashen Afirka a dukkanin fannoni, wajibi ne a jinjinawa yadda Sin din ke fadada tallafin da take baiwa kasashen Afirka ta fuskoki da dama, kamar samar da yankunan raya masanaantu, da yankunan cinikayya maras shinge, da taimakon raya fasahohin noma na zamani da dai sauran su.

 

Kaza lika, ya zama dole a yabawa kasar Sin don gane da sabbin shirye-shiryen hadin gwiwa 10 da ta gabatar a baya bayan nan, don ingiza zamanantar da kasashen Afirka abokan tafiyarta, shirye-shiryen da ko shakka babu za su yaukaka dunkulewar ayyukan hadin kan sassan biyu, kana sun dace da ajandar raya nahiyar Afirka ta nan zuwa shekarar 2063, da ma ajandar raya yankin cinikayya maras shinge na daukacin kasahen Afirka.

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
  • Sulaiman
    Shugaban Mongoliya Ya Zanta Da Ministan Wajen Kasar Sin

MASU ALAKA

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
Daga Birnin Sin

Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

June 14, 2026
Next Post
Babu Hannun Mijina A Wahalar Da Ƴan Nijeriya Ke Sha

Babu Hannun Mijina A Wahalar Da Ƴan Nijeriya Ke Sha

LABARAI MASU NASABA

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

June 15, 2026
An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.