• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Matan Arewa Da Suka Yi Fice (2)

by Bilkisu Tijjani
8 months ago
in Labarai
0
Wasu Matan Arewa Da Suka Yi Fice (2)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Aisha Yesufu

Aisha Yesufu ta kasance mai kokarin kare hakkin dan’Adam ce, sannan kuma tana kokari a fannin siyasa, kuma ta kasance ‘yar kasuwa ce, maia iyakar kokari akan ta ga ta yi adalci ko an yi wa mutum adalci, ta kasance tana cikin kungiyar nan da aka fi sani da ( Bring BackOurGirls,) Aannan ta ja hankalin mutanen duniya bayan dauke ‘yan matan Chibok sama da 200 da kungiyar ta’addanci ta Boko Haram ta yi a ranar 14 ga watan Afrilu 2014.

Aisha kuma wata jigo ce a masu zanga-zangar EndSaRS, ta nuna rashin amincewa da zaluncin ‘yansanda a Najeriya. Ta samu karbuwa sosai da ta yi haka.

  • What Women Hard anodized cookware Need within a Marriage
  • Sin Za Ta Samar Da Karin Matakai Daban Daban Na Tallafawa Tattalin Arziki

Kazalika tana daya daga cikin mata dari 100 na BBC a shekara ta 2020, kuma an saka su cikin manya dari 100 wadanda suka shahara a New African Magazine a wannan shekarar. A shekara ta 2023 Reputation Poll International ta amince da ita da a matsayin daya daga cikin ‘yan Afirika 100 da suka yi fice, sannan ta kasance cikin jerin mutane 50 da suka yi fice a ranar mata ta duniya a shekara 2023. Shawarar da Aisha ta bayar na ci gaba da da zaburar da mutane da yawa a fagen fafutukar kare hakkin dan‘Adam da adalci na zamantakewa.

Halima Buba

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Halima Buba ‘yar kasuwa kuma ma’aikaciyar banki ce tana matsayin Manajan Darakta kuma shugaba a Bankin Sun Trust bank Plc, ta samu wannan matsayin a Janairu 2021. Kafin wannan mukamin, ta kasance Mataimakiyar Manaja a Ecobank Nigeria.

Ta yi kyakkyawan aiki da ya shafi manyan cibiyoyin hada-hadar kudi ciki har da ‘ Allstates Trust Bank’ , Zenith Bank, Inland Bank Plc, Oceanic Bank Plc, da Ecobank Nigeria Limited. Halima Buba tana cikin wadanda suka samu kwarewa a fannin aikin banki. Bayan aikinta na banki, ta kasance mai ba da shawara ga matasa ga mata kuma ta himmatu wajen ci gaba da ba da ilimin a Nijeriya.

Lami Tumaka

Lami Tumaka ta kasance kwararriyar ko kuma wadda ta iya hulda da jama’a, mai gudanarwa, kuma mai magana da jama’a ce tafi shekaru 30 da kwarewa. Kwarewarta a fannin hulda da jama’a ta bayyana a lokacin da take rike da mukamin manajan hulda da jama’a na kamfanin Peugeot Automobile Nigeria (PAN) Limited, inda ta taka rawar gani wajen daukaka martabar kamfanin.

Kwazon da Tumaka ta nuna daga baya ya kai ta hukumar kula da harkokin jiragen ruwa ta kasa (wanda a yanzu ake kira NIMASA), inda ta yi aiki na tsawon shekaru 22, daga karshe ta kai matsayin Darakta kafin ta yi ritaya ta yi shuhura a sana’arta, ta sami lambobin yabo da yawa, ciki har da watsa labarai ta maritime na shekarar.

Iman Sulaiman Ibrahim

Imaan Sulaiman-Ibrahim fitacciyar ‘yar siyasa ce kuma ‘yar kasuwa mace wacce ta shahara wajen bayar da gudunmawar da ta bayar wajen yi wa gwamnati hidima da gudanar da mulki. Da farko ta rike mukamin Darakta a hukumar hana fataucin bil’ Adama ta kasa (NAPTIP) daga ranar 1 ga Disamba, 2020, zuwa ranar 27 ga Mayu, 2021, daga nan kuma shugaba Muhammadu Buhari ya ba ta mukamin kwamishina ta tarayya ga ‘yan gudun hijira, Baki, da mutunen cikin gida.

Imaan ta kasance da ita aka hada gwiwa kuma shugabar BumbleeBee Cibic Initiatibe, wadda aka fi sani da The Beehibe Initiatibe, wani dandali da aka sadaukar don ciyarwa da horar da mata masu ra’ayin siyasa da fahimtar da jama’a. Ta kuma yi aiki a matsayin mai ba da shawara ta musamman kan dabarun sadarwa ga Karamin Ministan Ilimi, Chukwuemeka Nwajiuba, sannan Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya A. A. Sule, a Satumba 2019.

A watan Yulin 2023, Imaan ta kafa tarihi a matsayin mace ta farko a harkokin ‘yan sanda, wadda shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada. Sannan tana nuna kwarewarta ga hidimar jama’a Sana’ar ta na da karfafawa mata da hada kan jama’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Matan ArewaArewaMata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Muka Sanya Tinubu Ya Soke Kwangilar Aikin Hanyar Kankara Zuwa Katsina inji Ibrahim Masari 

Next Post

An Kama Wani Matashi A Jigawa Saboda Ƙona Kakarsa

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

3 hours ago
Arewa
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

4 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

5 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

8 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

11 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

11 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Matashi A Jigawa Saboda Ƙona Kakarsa

LABARAI MASU NASABA

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Arewa

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.