• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Sam Nda-Isaiah Ta Miƙa Miliyan 250 Da Gwamna Bago Ya Ba Ɗan Adaidaita Sahun Kano

byNaziru Adam Ibrahim
12 months ago
Sam

Gidauniyar Sam Nda-Isaiah, ta gabatar da cakin Naira miliyan 250 da Gwamnan Jihar Neja Mohammed Umar Bago, ya bayar domin bai wa direban Adaidaita Sahu, Auwalu Salisu, mazaunin Kano, da ya zama gwarzon matashin kamfanin “LEADERSHIP” na shekarar 2023 bayan tsintar Naira miliyan 15 a babur dinsa kuma mayar ga masu shi.

Babban Editan Jaridar “LEADERSHIP”, Mista Azu Ishiekwene, wanda kuma darakta ne a gidauniyar Sam Nda-Isaiah, shi ya miƙa wa Salisu caki a shalkwatar Kamfanin, bisa shaidawar kawun Salisu, Abba Tukur, da kuma Babban Manajan Gidan Rediyo Arewa, Shehu Bala Kabara.

  • Ba Zan Ce Komai Game Da Rikicin NNPP Ba – Kwankwaso
  • Dole Ne A Tauna Tsakuwa Don Aya Ta Ji Tsoro

Bayan ya miƙa wa Salisu cakin, Ishiekwene ya bayyana godiya ga Gwamna Bago, bisa wannan gudummawar da ya bayar tare da yaba wa wanda ya karɓi cakin na nuna irin wannan abin ban mamaki ta ɗabi’ar gaskiya tare da shawartarsa na ya yi amfani da kuɗaɗen ta hanyar da ta dace.

Cikin jawabinsa a madadin Salisu, Kabara ya jinjina wa kamfanin LEADERSHIP na karramawar da gudunmawar Gwamna Bago, inda ya yi alƙawarin za a yi amfani da kudaden ta hanyar da ya kamata.

Gwamna Bago, ya yi wa Salisu, alƙawarin kyautar Naira miliyan 250 a madadin Shugaba Tinubu da muƙarrabansa da Ƙungiyar Gwamnonin APC, yayin taron shekara-shekara na kamfanin LEADERSHIP.

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Daga baya aka gabatar da Salisu a matsayin gwarzon matashin kamfanin jaridar na 2023 saboda halin gaskiyarsa, gwamnan ya cika alkawarin da ya yi wa Salisu ta hannun Gidauniyar Sam Nda-Isaiah.

Matashin Salisu ya kuma samu tallafin karatu a Jami’ar Baze da ke birnin tarayya Abuja, har zuwa matakin digirin digirgir, daga ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023, Peter Obi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Ingila Ta Dauki Thomas Tuchel A Matsayin Sabon Kocinta

Ingila Ta Dauki Thomas Tuchel A Matsayin Sabon Kocinta

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version