Yau Juma’a da safe, ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar Sin ya kira taron manema labarai, inda ya yi bayyani kan yanayin tafiyar tattalin arzikin al’umma daga watan Janairu zuwa Satumban bana. Alkaluman da hukumar kididdiga ta bayar na nuna cewa, yawan GDPn kasar Sin daga watan Janairu zuwa Satumban bana, ya kai fiye da dala triliyan 13, abin da ya karu da kashi 4.8% kan na makamancin lokacin a bara, bisa darajar kudi wancan lokaci.
Ban da wannan kuma, a wannan lokaci, yawan karuwar darajar masana’antu ya kai kashi 5.8% bisa na makamancin lokaci a bara, wanda shi ne muhimmin ma’aunin bunkasuwar tattalin arzikin kasa. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp