• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Masar Da Iran

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Masar Da Iran
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na kasar Masar Abdel Fattah al Sisi a daren jiya Laraba a Kazan na Rasha, yayin da yake halartar taron shugabannin BRICS.

 

Xi ya taya Masar murnar shiga taron a matsayin mamba a karon farko. Ya kuma jaddada cewa, ya kamata bangarorin biyu su kara azama wajen raya dangantakarsu zuwa huldar kafa kyakkyawar makomarsu ta bai daya a zabon zamani. Sin na fatan kara hadin gwiwa da Masar don ingiza bunkasuwar kasashen BRICS mai dorewa da karfafa karfin kasashe masu tasowa da masu saurin bunkasuwa, da ma kiyaye muradun kasashe masu tasowa.

  • An Gudanar Da Taron Tattaunawar Kafofin Watsa Labarai Na Kazan Na Kasashen BRICS
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawar Kafofin Watsa Labarai Na Kazan Na Kasashen BRICS

A nasa bangaren, Abdel Fattah al Sisi ya nuna godiya ga goyon bayan da Sin ta nunawa kasarsa wajen shiga tsarin BRICS. Yana mai fatan kara tuntubar kasashen biyu a mabambantan bangarori, da ma kiyaye muradun kasashe masu tasowa da masu saurin bunkasuwa cikin hadin kai, da kuma ingiza kafa tsarin daidaita harkokin duniya bisa adalci da daidaici.

 

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Ban da wannan kuma, bangarorin biyu sun yi musanyar ra’ayi game da halin da ake ciki a yankin gabas ta tsakiya. A ganin Xi, batun Palasdinu muhimmin batu ne ga matsalar gabas ta tsakiya. Abin da ake sa gaba shi ne, a yi iyakacin kokarin aiwatar da kudurorin da aka zartas a yayin tarukan kwamitin sulhu na MDD, da gaggauta tsagaita bude wuta a wurin. Tabbatar da tsarin “kafa kasashe biyu” ita ce hanya daya tilo da za a bi wajen warware wannan matsala bisa adalci a duk fannoni mai dorewa.

 

Kazalika, an ba da labari cewa, a wannan rana da yamma, Xi ya gana da takwaransa na kasar Iran Masoud Pezeshkian. Yayin ganawar tasu, Xi ya nanata cewa, Sin ba za ta sauya matsayinta na sada zumunta da hadin gwiwarta da Iran ba, duk da sauye-sauyen yanayi da ake fuskanta a shiyya-shiyya da ma duk duniya baki daya. A nasa bangaren kuwa, Pezeshkian ya ce, Iran na fatan ita da kasar Sin za su goyi wa juna baya kan wasu muradu masu tushe na kasashen biyu, da ma yaki da babakere tare. Yana godiya ga goyon bayan da Sin take nunawa kasar na shiga tsarin BRICS. Yana mai fatan kara hadin gwiwarta da Sin mai zurfi a dandaloli masu gudanar da harkoki tsakanin bangarori daban-daban ciki har da BRICS. (Amina Xu)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Katsewar Wutar Lantarki Ta Arewa: Akwai Yiwuwar Korar Ma’aikata Bayan Kamfanoni Sun Yi Asara Sama Da Biliyan 100

Next Post

Ministan Tsaro Ya Jinjina Wa Gwamnan Zamfara, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen ‘Yan Bindiga 

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

2 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

3 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

5 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

8 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

9 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

10 hours ago
Next Post
Ministan Tsaro Ya Jinjina Wa Gwamnan Zamfara, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen ‘Yan Bindiga 

Ministan Tsaro Ya Jinjina Wa Gwamnan Zamfara, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen 'Yan Bindiga 

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.