ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Tsaro Ya Jinjina Wa Gwamnan Zamfara, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen ‘Yan Bindiga 

by Hussein Yero and Sulaiman
2 years ago
ZAMFARA

Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar, ya yaba wa Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal bisa jajircewarsa da ci gaba da bayar da goyon baya ga ayyukan soji a jihar.

 

A ranar Alhamis ɗin nan ne ministan ya ziyarci gidan gwamnatin Zamfara da hedikwatar rundunar haɗin gwiwa ta ‘Operation Fansar Yamma’ da ke Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Masar Da Iran
  • TCN Ta Gano Dalilin Katsewar Wutar Lantarki A Arewacin Nijeriya, Ta Fara Gyara

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa ziyarar na da nufin inganta haɗin gwiwa tsakanin jihar da ma’aikatar tsaro.

 

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Sanarwar ta ƙara da cewa, ministan ya tattauna batutuwan da suka shafi ziyarar da gwamna Lawal da gwamna Raɗɗa suka kai Ma’aikatar Tsaro a farkon makon nan.

 

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya jaddada aniyar gwamnatinsa na bayar da haɗin kai ga dukkanin hukumomin tsaro domin tabbatar da zaman lafiya a Zamfara.

 

“Ina so in miƙa godiyata ga Ministan Tsaro, wanda ya zo yau domin tattauna batun matsalar tsaro a Zamfara.

 

“Kwanaki kaɗan da suka gabata ni da gwamnan jihar Katsina muka je ofishin minista a Ma’aikatar Tsaro, inda muka tattauna batutuwa masu muhimmanci.

 

“Bayan kwana biyu, ministan ya zo wurinmu. Wannan abin a yaba ne na irin ƙwazon da ministan ya nuna.

 

“Zamfara na fuskantar ƙalubalen tsaro da dama, amma a matsayinmu na gwamnati mai cikakken iko, duk mun tashi tsaye don neman taimako da haɗa kai da hukumomin tsaro. Mun himmatu wajen ba da dukan taimako ga sojoji.

 

“Za mu kai yaƙi ne ga ‘yan bindigar saboda kare kanmu. Abin da na gani zuwa yanzu ya nuna cewa batun ‘yan bindiga zai zama tarihi in Allah Ya yarda.

 

“Na yi alƙawari ga ministan. Bugu da ƙari, na saya wa sojoji motocin da harsashi ba ya fasa su guda goma. Haka kuma akwai sauran kayan aikin da za a ba jami’an tsaro domin taimaka musu wajen yaƙar ‘yan bindiga.

 

“Idan za mu iya magance ƙalubalen ‘yan bindiga a Zamfara, za a magance kashi 90 na matsalar jihar.

 

“Ina kira ga jami’an tsaro, musamman sojoji, cewa muna buƙatar su. Ina da yaƙinin suna da abin da ake buƙata don kawar da ‘yan ta’adda.

 

“Na yi alƙawari, kuma ina tare da ku. Ina godiya ga kowa da kowa, musamman Minista da ke ba da lokacin zama tare da mu.”

 

A farko dai, Ministan Tsaro, Alhaji Badaru Abubakar, ya ce nasarorin da ake samu a yaƙi da ‘yan bindiga na da alaƙa da ci gaba da goyon bayan gwamnatin Gwamna Lawal.

 

“Mun fara ganin an samu ci gaba, sakamakon goyon bayan Gwamnan Jihar Zamfara.

 

“Gwamnan ya samar da masauki ga kwamandojin soji, wuraren horo, kyamarori masu sa ido na nesa, motoci, da dai sairan kayan aiki. Har ma ya bai wa sojojin motocin yaƙi. Ranka ya daɗe, mun gode maka sosai.”

ZAMFARA
Hussein Yero
+ posts Bio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Matawalle Ya Buƙaci Magoya Bayansa Su Mara Wa Shugaba Tinubu, Gwamna Lawal Baya
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Majalisar Zamfara Ta Dakatar Da Shugabannin Kananan Hukumomi Biyu Kan Zargin Almundahanar Kuɗaɗe
ZAMFARA
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Fashewar Tankar Mai A Jigawa: Remi Tinubu Ta Bayar Da Gudunmawar Miliyan ₦40m Da Kayayyakin Abinci

Fashewar Tankar Mai A Jigawa: Remi Tinubu Ta Bayar Da Gudunmawar Miliyan ₦40m Da Kayayyakin Abinci

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.