ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Tsaro Ya Jinjina Wa Gwamnan Zamfara, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen ‘Yan Bindiga 

by Hussein Yero and Sulaiman
2 years ago
ZAMFARA

Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar, ya yaba wa Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal bisa jajircewarsa da ci gaba da bayar da goyon baya ga ayyukan soji a jihar.

 

A ranar Alhamis ɗin nan ne ministan ya ziyarci gidan gwamnatin Zamfara da hedikwatar rundunar haɗin gwiwa ta ‘Operation Fansar Yamma’ da ke Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Masar Da Iran
  • TCN Ta Gano Dalilin Katsewar Wutar Lantarki A Arewacin Nijeriya, Ta Fara Gyara

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa ziyarar na da nufin inganta haɗin gwiwa tsakanin jihar da ma’aikatar tsaro.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Sanarwar ta ƙara da cewa, ministan ya tattauna batutuwan da suka shafi ziyarar da gwamna Lawal da gwamna Raɗɗa suka kai Ma’aikatar Tsaro a farkon makon nan.

 

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya jaddada aniyar gwamnatinsa na bayar da haɗin kai ga dukkanin hukumomin tsaro domin tabbatar da zaman lafiya a Zamfara.

 

“Ina so in miƙa godiyata ga Ministan Tsaro, wanda ya zo yau domin tattauna batun matsalar tsaro a Zamfara.

 

“Kwanaki kaɗan da suka gabata ni da gwamnan jihar Katsina muka je ofishin minista a Ma’aikatar Tsaro, inda muka tattauna batutuwa masu muhimmanci.

 

“Bayan kwana biyu, ministan ya zo wurinmu. Wannan abin a yaba ne na irin ƙwazon da ministan ya nuna.

 

“Zamfara na fuskantar ƙalubalen tsaro da dama, amma a matsayinmu na gwamnati mai cikakken iko, duk mun tashi tsaye don neman taimako da haɗa kai da hukumomin tsaro. Mun himmatu wajen ba da dukan taimako ga sojoji.

 

“Za mu kai yaƙi ne ga ‘yan bindigar saboda kare kanmu. Abin da na gani zuwa yanzu ya nuna cewa batun ‘yan bindiga zai zama tarihi in Allah Ya yarda.

 

“Na yi alƙawari ga ministan. Bugu da ƙari, na saya wa sojoji motocin da harsashi ba ya fasa su guda goma. Haka kuma akwai sauran kayan aikin da za a ba jami’an tsaro domin taimaka musu wajen yaƙar ‘yan bindiga.

 

“Idan za mu iya magance ƙalubalen ‘yan bindiga a Zamfara, za a magance kashi 90 na matsalar jihar.

 

“Ina kira ga jami’an tsaro, musamman sojoji, cewa muna buƙatar su. Ina da yaƙinin suna da abin da ake buƙata don kawar da ‘yan ta’adda.

 

“Na yi alƙawari, kuma ina tare da ku. Ina godiya ga kowa da kowa, musamman Minista da ke ba da lokacin zama tare da mu.”

 

A farko dai, Ministan Tsaro, Alhaji Badaru Abubakar, ya ce nasarorin da ake samu a yaƙi da ‘yan bindiga na da alaƙa da ci gaba da goyon bayan gwamnatin Gwamna Lawal.

 

“Mun fara ganin an samu ci gaba, sakamakon goyon bayan Gwamnan Jihar Zamfara.

 

“Gwamnan ya samar da masauki ga kwamandojin soji, wuraren horo, kyamarori masu sa ido na nesa, motoci, da dai sairan kayan aiki. Har ma ya bai wa sojojin motocin yaƙi. Ranka ya daɗe, mun gode maka sosai.”

ZAMFARA
Hussein Yero
+ posts Bio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    ’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara
ZAMFARA
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
  • Sulaiman
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
  • Sulaiman
    Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita
  • Sulaiman
    Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano
Labarai

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci
Labarai

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Labarai

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Next Post
Fashewar Tankar Mai A Jigawa: Remi Tinubu Ta Bayar Da Gudunmawar Miliyan ₦40m Da Kayayyakin Abinci

Fashewar Tankar Mai A Jigawa: Remi Tinubu Ta Bayar Da Gudunmawar Miliyan ₦40m Da Kayayyakin Abinci

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.