• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wa Ke Da Gaskiya Tsakanin NDLEA Da Sanata Ashiru? 

by Khalid Idris Doya
12 months ago
in Labarai
0
Wa Ke Da Gaskiya Tsakanin NDLEA Da Sanata Ashiru? 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi a Nijeriya (NDLEA) ta ce, dan majalisa daga Jihar Kwara kuma mataimakin shugaban masu rinjaye a majalisar dattawa, Oyeyola Ashiru, ya farmaki ayyukanta ne saboda kwato wasu miyagun kwayoyi a gidansa.  

A yayin zaman majalisar na ranar 15 ga Octoba, dan majalisar ya ce, “NDLEA ta kasance hukuma mai cin hanci da rashawa.” don haka ya yi kira da a samar da wata sabowar hukumar da za dunga yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi.

  • Abin Da Ya Sa Ƙasashen Duniya Suka Gina Majalisar Ɗinkin Duniya – Sakatare Janar
  • Super Eagles Ta Hauro Matsayi Na 36 A Jadawalin Duniya Na FIFA

Ya yi kiran ne a kan kudurin neman kafa cibiyar wayar da kai kan ta’ammuli da kwayoyi da gyaran hali ta kasa.

Sai dai bayan furucin nasa, NDLEA ta mayar da zazzafan martani a gareshi.

Shugaban hukumar NDLEA, Buba Marwa ya ce, fushin da sanatan ya yi ya fito ne sakamakon kullin da ke ransa kuma babu kanshin gaskiya a lamarin.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Da yake ganawa da ‘yan jarida ta bakin kakakin hukumar, Femi Babafemi, ya ce NDLEA ta dukufa wajen gudanar da ayyukan da suke kanta na dakile sha da fataucin miyagun kwayoyi ciki kuwa har da wani kame da ta yi a gidan sanatan.

Babafemi ya ce hukumar ta jira na tsawon mako guda domin dan majalisar ya fayyace matsayar kan wannan zargi da kazafin.

Ya ce, dole ne a garesu su fito su fayyace zare da abawa kan furucin sanatan, “Tabbas ba shakka kafa wata hukuma na wuyan majalisa, amma in an gayyacemu domin mu bayar da namu gudunmawar za mu bayar, za mu bayyana matsayarmu.”

Sai dai ya ce ba kuma za su zura ido wani sanata ya fito ya yi ta sharara batun da babu tushe a kansu ba kuma su yi shiru da bakinsu.

Ya bayar da labarin yadda aka yi sanatan ya fara fushi da su, “Kwanakin baya a wani gidan sanatan da ke GRA Ilorin a Jihar Kwara, mun kamo miyagun kwayoyi tare da kama wasu mukarraban sanatan su biyu, Ibrahim Mohammed da Muhammed Yahaya.

“Bisa bayanan sirri da muka samu ya tabbatar mana cewa gidan sanatan ya kasance wata dandamalin hada-hadar miyagun kwayoyi a tsakanin dillalai da masu amfani da shi. Don haka ne jami’anmu suka yi dirar mikiya a gidan da karfe 1:30 na dare a ranar 4 ga watan Fabrairun 2024, inda muka kama hadiminsa biyu, dayan na ukun kuma ya ari na kare,” Babafemi ya shaida.

Ya ce ba a nan ma rigimar tasu ta tsaya ba, “A wani takun tsaka da sanatan, hukumar ta kuma amshi wani rahoton sirri da ke cewa wasu yaran sanatan da aka fi sani da ‘Omo Senator’ wadanda suke amfani da gudanar da ayyukansu daga yankinsa, Offa, su ma suna hada-hadar miyagun kwayoyi. Mun kai samame a wata mahadarsu da ke Offa, inda daya daga cikinsu Oluwatosin Odepidan ya shiga hannu tare da miyagun kwayoyi a ranar 11 ga Yunin 2023.”

Sai dai jami’ar watsa labarai na sanatan, Hauwa Ahmad ta nuna takaicinsa kan irin zargin da hukumar ke yi wa sanatan. Ya ce, Sanata Ashiru na da ikon bayar da gudunmawar kan kowace kuduri da ke gaban majalisar. Don haka ta nuna cewa ya nemi a kafa wata hukuma bai dace NDLEA ta fusata ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AshiruNDLEASanata
ShareTweetSendShare
Previous Post

CBN Ya Ƙi Amince Wa Da Umarnin Majalisa Kan Dakatar Da Amfani Da Tsofaffin Naira

Next Post

Hatsarin Jirgi Ya Sa Mataimakin Shugaban Kasa Ya Soke Ziyarar Amurka

Related

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara
Tsaro

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

1 hour ago
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa
Labarai

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

2 hours ago
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya
Labarai

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

3 hours ago
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC
Labarai

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

4 hours ago
Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya
Labarai

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

7 hours ago
Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa
Labarai

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

8 hours ago
Next Post
Hatsarin Jirgi Ya Sa Mataimakin Shugaban Kasa Ya Soke Ziyarar Amurka

Hatsarin Jirgi Ya Sa Mataimakin Shugaban Kasa Ya Soke Ziyarar Amurka

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

October 5, 2025
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

October 5, 2025
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.