ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wa Ke Da Gaskiya Tsakanin NDLEA Da Sanata Ashiru? 

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Ashiru

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi a Nijeriya (NDLEA) ta ce, dan majalisa daga Jihar Kwara kuma mataimakin shugaban masu rinjaye a majalisar dattawa, Oyeyola Ashiru, ya farmaki ayyukanta ne saboda kwato wasu miyagun kwayoyi a gidansa.  

A yayin zaman majalisar na ranar 15 ga Octoba, dan majalisar ya ce, “NDLEA ta kasance hukuma mai cin hanci da rashawa.” don haka ya yi kira da a samar da wata sabowar hukumar da za dunga yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi.

  • Abin Da Ya Sa Ƙasashen Duniya Suka Gina Majalisar Ɗinkin Duniya – Sakatare Janar
  • Super Eagles Ta Hauro Matsayi Na 36 A Jadawalin Duniya Na FIFA

Ya yi kiran ne a kan kudurin neman kafa cibiyar wayar da kai kan ta’ammuli da kwayoyi da gyaran hali ta kasa.

ADVERTISEMENT

Sai dai bayan furucin nasa, NDLEA ta mayar da zazzafan martani a gareshi.

Shugaban hukumar NDLEA, Buba Marwa ya ce, fushin da sanatan ya yi ya fito ne sakamakon kullin da ke ransa kuma babu kanshin gaskiya a lamarin.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Da yake ganawa da ‘yan jarida ta bakin kakakin hukumar, Femi Babafemi, ya ce NDLEA ta dukufa wajen gudanar da ayyukan da suke kanta na dakile sha da fataucin miyagun kwayoyi ciki kuwa har da wani kame da ta yi a gidan sanatan.

Babafemi ya ce hukumar ta jira na tsawon mako guda domin dan majalisar ya fayyace matsayar kan wannan zargi da kazafin.

Ya ce, dole ne a garesu su fito su fayyace zare da abawa kan furucin sanatan, “Tabbas ba shakka kafa wata hukuma na wuyan majalisa, amma in an gayyacemu domin mu bayar da namu gudunmawar za mu bayar, za mu bayyana matsayarmu.”

Sai dai ya ce ba kuma za su zura ido wani sanata ya fito ya yi ta sharara batun da babu tushe a kansu ba kuma su yi shiru da bakinsu.

Ya bayar da labarin yadda aka yi sanatan ya fara fushi da su, “Kwanakin baya a wani gidan sanatan da ke GRA Ilorin a Jihar Kwara, mun kamo miyagun kwayoyi tare da kama wasu mukarraban sanatan su biyu, Ibrahim Mohammed da Muhammed Yahaya.

“Bisa bayanan sirri da muka samu ya tabbatar mana cewa gidan sanatan ya kasance wata dandamalin hada-hadar miyagun kwayoyi a tsakanin dillalai da masu amfani da shi. Don haka ne jami’anmu suka yi dirar mikiya a gidan da karfe 1:30 na dare a ranar 4 ga watan Fabrairun 2024, inda muka kama hadiminsa biyu, dayan na ukun kuma ya ari na kare,” Babafemi ya shaida.

Ya ce ba a nan ma rigimar tasu ta tsaya ba, “A wani takun tsaka da sanatan, hukumar ta kuma amshi wani rahoton sirri da ke cewa wasu yaran sanatan da aka fi sani da ‘Omo Senator’ wadanda suke amfani da gudanar da ayyukansu daga yankinsa, Offa, su ma suna hada-hadar miyagun kwayoyi. Mun kai samame a wata mahadarsu da ke Offa, inda daya daga cikinsu Oluwatosin Odepidan ya shiga hannu tare da miyagun kwayoyi a ranar 11 ga Yunin 2023.”

Sai dai jami’ar watsa labarai na sanatan, Hauwa Ahmad ta nuna takaicinsa kan irin zargin da hukumar ke yi wa sanatan. Ya ce, Sanata Ashiru na da ikon bayar da gudunmawar kan kowace kuduri da ke gaban majalisar. Don haka ta nuna cewa ya nemi a kafa wata hukuma bai dace NDLEA ta fusata ba.

Ashiru
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Hatsarin Jirgi Ya Sa Mataimakin Shugaban Kasa Ya Soke Ziyarar Amurka

Hatsarin Jirgi Ya Sa Mataimakin Shugaban Kasa Ya Soke Ziyarar Amurka

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.