• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin Ma’aikatan NAFDAC Ya Kazanta Halin Da Masana’antun Harhada Magunguna Ke Ciki

by Abubakar Abba
1 year ago
Yajin Aiki

Shugaban kungiyar masu sarrafa magunguna na kasa Oluwatosin Jolayemi ya bayyana cewa, yajin aikin da jami’an hukumar kula da inaganci abinci da magunguna ta Kasa ke ci gaba da yi, ya kara janyo masana’atun gaza kwashe kayansu da suka shigo da su cikin kasar daga tashoshin Jiragen ruwan kasar.

Jolayemi ya zayyano manyan ilolin da yajin aikin ya janyo masu sarrafa magungunan, musamman na masana’atun gazawar su ta kwashe kayansu da suka shigo da su cikin kasar daga tashoshin Jiragen ruwan kasar.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • ‘Yan Bindiga Ba Su Karɓe Sansanin Horo Da Ke Neja Ba – Hedikwatar Tsaro

A cewarsa, iadan har masu sarrafa magungunan, ba su samu amincewar hukumar kula da inganci abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ba, to fa, ba za su iya kwashe kayansu daga tashoshin Jiragen ruwan kasar ba.

Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa, yajin aikin jami’an hukumar ya kara tabarbarar da fannin kiwon lafiyar kasar nan, wanda a yanzu, hakan ya jefa fargaba a zukantan ‘yan kasar, a kan inganci magungunan da ake shigowa da su, cikin kasar.

Jami’an hukumar sun tsunduma cikin yajin aikin na sai baba ta gani ne, a karkashin kungiyar manyan ma’aikata da kamfanoni mallakar gwamnati (SSASCGOC) a ranar 7 na watan Okutobar 2024.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

Sun tsunduma yajin aikin ne bisa neman a biya masu bukatunsu da suka hada da maido da sakamakon zana jarrabar karin girma ta 2024 a kan maki kashi 35.

Daya bukatar jami’an ita ce, cike guraben Daraktocin hukumar, ianganta tsarin jarrabawa da karin girma ga jami’in sanin halaiyyar ‘yan Adama da kuma biyan su karin albashin da ya kamata ace an biya su da aka dauke su aiki a na 2022.

Sai dai, Jolayemi ya jaddada cewa, kalubalen da masu sarrafa magungunan ke fuskanta, ta zarce yajin aikin da ma’aikatan hukumar NAFDAC, ke ci gaba da yi a yanzu.

A cewarsa, a zahiri maganar ba wai kawai dangane da hukumar ta NAFDAC ba ce, amma maganar ita ce, a kan rashin iya biyan kudaden fiton kayan su da ke a tashoshin Jiragen ruwa na kasar, saboda kalubalen da suka shafi bankuna

Jolayemi ya ci gaba da cewa, “Ko da kuwa hukumar NAFDAC ta warware matsalolinta da jami’anta, mu a namu bangaren za mu ci gaba da fuskantar manyan matsalolin mu na kasa biyan kudaden na fiton kayan mu.”

A cewarsa,“Tun daga kan manya masana’antu masu sarrafa magunguna da kuma kananansu yajin aikin jami’an hukumar ta NAFDAC, ya shafi gudanar da ayyuaknsu.”

Shi ma a na sa bangaren tsohon shugaban kungiyar masu sa ido a kan yadda ake sarrafa magunguna ta kasa (PSN) Olumide Akintayo, ya nuna damuwarsa a kan yajin aikin jami’an na hukumar NAFDAC.

Olumide ya yi nuni da cewa, yajin akin zai zai janyo tsaiko wajen rabar da magunguna a kasar da kuma shigowar magunguna marasa inganci cikin kasar Kazalika ya ce, yajin aikin zai yanyo jinkiri, wajen daukar samfarin magungunna da za a yi gwajinsu a dakin gwaje-gwaje na hukumar NAFDAC, duba da cewa, har yanzu, magungunna da masu sarrafa magungunan suka shigo da su cikin kasar, na jibge a tashoshin Jiragen rawa na kasar.

Ya yi gargadin cewa, yajin aikin zai kara tabarbarar da tafiyar shugabancin da hukumar idan har, ba a yi masalaha ba.

Ya yi kira ga Darakta Janar ta hukumar NAFDAC ta kasa Farfesa Mojisola Adeyeye, da ta lalubo da mafita da jami’anta kan yajin aikin, duba da yadda yajin aikin, ke neman yiwa fannin kiwon lafiyar kasar nakasu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

October 25, 2025
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

October 25, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA
Tattalin Arziki

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Next Post
Yajin Aiki

Kakakin Ma'aikatar Tsaron Sin Ya Yi Tir Da Sayar Da Makamai Da Amurka Ke Yi Wa Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.