• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin Ma’aikatan NAFDAC Ya Kazanta Halin Da Masana’antun Harhada Magunguna Ke Ciki

by Abubakar Abba
8 months ago
in Tattalin Arziki
0
Yajin Aikin Ma’aikatan NAFDAC Ya Kazanta Halin Da Masana’antun Harhada Magunguna Ke Ciki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kungiyar masu sarrafa magunguna na kasa Oluwatosin Jolayemi ya bayyana cewa, yajin aikin da jami’an hukumar kula da inaganci abinci da magunguna ta Kasa ke ci gaba da yi, ya kara janyo masana’atun gaza kwashe kayansu da suka shigo da su cikin kasar daga tashoshin Jiragen ruwan kasar.

Jolayemi ya zayyano manyan ilolin da yajin aikin ya janyo masu sarrafa magungunan, musamman na masana’atun gazawar su ta kwashe kayansu da suka shigo da su cikin kasar daga tashoshin Jiragen ruwan kasar.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • ‘Yan Bindiga Ba Su Karɓe Sansanin Horo Da Ke Neja Ba – Hedikwatar Tsaro

A cewarsa, iadan har masu sarrafa magungunan, ba su samu amincewar hukumar kula da inganci abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ba, to fa, ba za su iya kwashe kayansu daga tashoshin Jiragen ruwan kasar ba.

Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa, yajin aikin jami’an hukumar ya kara tabarbarar da fannin kiwon lafiyar kasar nan, wanda a yanzu, hakan ya jefa fargaba a zukantan ‘yan kasar, a kan inganci magungunan da ake shigowa da su, cikin kasar.

Jami’an hukumar sun tsunduma cikin yajin aikin na sai baba ta gani ne, a karkashin kungiyar manyan ma’aikata da kamfanoni mallakar gwamnati (SSASCGOC) a ranar 7 na watan Okutobar 2024.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Sun tsunduma yajin aikin ne bisa neman a biya masu bukatunsu da suka hada da maido da sakamakon zana jarrabar karin girma ta 2024 a kan maki kashi 35.

Daya bukatar jami’an ita ce, cike guraben Daraktocin hukumar, ianganta tsarin jarrabawa da karin girma ga jami’in sanin halaiyyar ‘yan Adama da kuma biyan su karin albashin da ya kamata ace an biya su da aka dauke su aiki a na 2022.

Sai dai, Jolayemi ya jaddada cewa, kalubalen da masu sarrafa magungunan ke fuskanta, ta zarce yajin aikin da ma’aikatan hukumar NAFDAC, ke ci gaba da yi a yanzu.

A cewarsa, a zahiri maganar ba wai kawai dangane da hukumar ta NAFDAC ba ce, amma maganar ita ce, a kan rashin iya biyan kudaden fiton kayan su da ke a tashoshin Jiragen ruwa na kasar, saboda kalubalen da suka shafi bankuna

Jolayemi ya ci gaba da cewa, “Ko da kuwa hukumar NAFDAC ta warware matsalolinta da jami’anta, mu a namu bangaren za mu ci gaba da fuskantar manyan matsalolin mu na kasa biyan kudaden na fiton kayan mu.”

A cewarsa,“Tun daga kan manya masana’antu masu sarrafa magunguna da kuma kananansu yajin aikin jami’an hukumar ta NAFDAC, ya shafi gudanar da ayyuaknsu.”

Shi ma a na sa bangaren tsohon shugaban kungiyar masu sa ido a kan yadda ake sarrafa magunguna ta kasa (PSN) Olumide Akintayo, ya nuna damuwarsa a kan yajin aikin jami’an na hukumar NAFDAC.

Olumide ya yi nuni da cewa, yajin akin zai zai janyo tsaiko wajen rabar da magunguna a kasar da kuma shigowar magunguna marasa inganci cikin kasar Kazalika ya ce, yajin aikin zai yanyo jinkiri, wajen daukar samfarin magungunna da za a yi gwajinsu a dakin gwaje-gwaje na hukumar NAFDAC, duba da cewa, har yanzu, magungunna da masu sarrafa magungunan suka shigo da su cikin kasar, na jibge a tashoshin Jiragen rawa na kasar.

Ya yi gargadin cewa, yajin aikin zai kara tabarbarar da tafiyar shugabancin da hukumar idan har, ba a yi masalaha ba.

Ya yi kira ga Darakta Janar ta hukumar NAFDAC ta kasa Farfesa Mojisola Adeyeye, da ta lalubo da mafita da jami’anta kan yajin aikin, duba da yadda yajin aikin, ke neman yiwa fannin kiwon lafiyar kasar nakasu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NAFDACYajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ta Samar Ta Hanyar Dogaro Da Makamashi Mai Tsabta Ya Kai Kw/h Triliyan 2.51 Daga Watan Janairu Zuwa Satumba

Next Post

Kakakin Ma’aikatar Tsaron Sin Ya Yi Tir Da Sayar Da Makamai Da Amurka Ke Yi Wa Taiwan

Related

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

5 days ago
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

4 weeks ago
Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

1 month ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

1 month ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

2 months ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

2 months ago
Next Post
Yajin Aiki

Kakakin Ma'aikatar Tsaron Sin Ya Yi Tir Da Sayar Da Makamai Da Amurka Ke Yi Wa Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

July 3, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.