• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karuwar Tattalin Arzikin Sin Ita Ce Damar Raya Ciniki A Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Karuwar Tattalin Arzikin Sin Ita Ce Damar Raya Ciniki A Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abokaina, idan akwai dama, za ku iya zuwa birnin Lagos a kwanaki masu zuwa don halartar wasu bukukuwan baje koli masu ban sha’awa.

 

Daga ranar 5 zuwa ta 8 ga watan nan da muke ciki, za a shirya wani bikin baje kolin kayayyaki a cibiyar Landmark Centre dake tsibirin Victoria na Lagos, inda kamfanonin Sin fiye da 250 za su halarta. An ce kayayyakin da za a nuna a wajen bikin sun hada da injunan aikin gona, da na’urori masu nasaba da samar da wutar lantarki, da tufafi, da abinci, da dai sauransu. Ban da haka, daga ranar 5 zuwa ta 7 ga watan Nuwamban da muke ciki, akwai wani bikin baje koli na daban da kamfanoni 56 na lardin Zhejiang na kasar Sin za su halarta, wanda zai gudana a cibiyar TBS dake kan tsibirin Lagos.

  • Zanga-zanga: Kotu Ta Bayar Da Belin Matasa 67 A Kan N670m
  • Matasa 5 Cikin Masu Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Sun yanke Jiki Sun Faɗi A Kotu

Wadannan bukukuwa za su kai kayayyakin Sin zuwa Afirka, kana a sa’i daya, wani bikin baje kolin da zai gudana a kasar Sin, a nasa bangare zai kai dimbin kayayyakin Afirka zuwa kasuwar kasar Sin. Daga ranar 5 zuwa ta 10 ga watan Nuwamba, za a gudanar da bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su cikin kasar Sin daga ketare wato CIIE karo na 7 a birnin Shanghai na kasar Sin, inda za a nuna dimbin kayayyakin da kasar Sin take shigowa da su daga ketare, ciki har da kasashen Afirka, musamman ma bisa yarjeniyoyin da kasashen Afirka suka kulla da kasar Sin a wajen taron dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka da ya gudana a bana, misali gyadar Najeriya, da ruwan zuman kasar Rwanda, da waken gahawa na kasar Burundi, gami da kifayen kasar Madagascar, da dai sauransu.

 

Labarai Masu Nasaba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

Wadannan bukukuwan da za su gudana sun nuna yanayi mai armashi na cudanyar Sin da Afirka a fannin tattalin arziki da na ciniki, kana wani babban dalilin da ya sa ake samun wannan yanayi mai kyau shi ne karuwar tattalin arzikin Sin, duba da cewa a watanni 9 na farko na bana, cinikin da aka yi tsakanin kasar Sin da sauran kasashe da yankuna fiye da 160 ya karu sosai, kana saurin karuwar jamillar GDP ta Sin yana kan gaba a cikin manyan tattalin arzikin duniya. Karuwar tattalin arzikin Sin, da karin matakan da gwamnatin kasar ta dauka don sa kaimi ga ci gaban tattalin arziki, sun sa kungiyoyin hada-hadar kudi irinsu Goldman Sachs, da JPMorgan Chase, da Swiss Bank, dukkansu sun daga matsayin hasashen da suka yi dangane da karuwar tattalin arzikin Sin a bana.

 

Sai dai me ya sa karuwar tattalin arzikin Sin kan janyo ci gaban bangaren ciniki da tattalin arziki a kasashen Afirka? Dalili shi ne, kasar Sin ta dukufa wajen samar da damar raya tattalin arziki ga kasashe daban daban a yayin da take kokarin zamanantar da kanta, da kuma tabbatar da ci gaba na bai daya na daukacin kasashe masu tasowa. Wadannan matakai sun dace da manufar kasar ta gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkan bil Adam. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zanga-zanga: Kotu Ta Bayar Da Belin Matasa 67 A Kan N670m

Next Post

Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Related

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

3 days ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

3 days ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

4 days ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

5 days ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

6 days ago
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama
Ra'ayi Riga

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

6 days ago
Next Post
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

September 8, 2025
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

September 8, 2025
Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

September 8, 2025
Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

September 8, 2025
Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.