ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karuwar Tattalin Arzikin Sin Ita Ce Damar Raya Ciniki A Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Sin

Abokaina, idan akwai dama, za ku iya zuwa birnin Lagos a kwanaki masu zuwa don halartar wasu bukukuwan baje koli masu ban sha’awa.

 

Daga ranar 5 zuwa ta 8 ga watan nan da muke ciki, za a shirya wani bikin baje kolin kayayyaki a cibiyar Landmark Centre dake tsibirin Victoria na Lagos, inda kamfanonin Sin fiye da 250 za su halarta. An ce kayayyakin da za a nuna a wajen bikin sun hada da injunan aikin gona, da na’urori masu nasaba da samar da wutar lantarki, da tufafi, da abinci, da dai sauransu. Ban da haka, daga ranar 5 zuwa ta 7 ga watan Nuwamban da muke ciki, akwai wani bikin baje koli na daban da kamfanoni 56 na lardin Zhejiang na kasar Sin za su halarta, wanda zai gudana a cibiyar TBS dake kan tsibirin Lagos.

ADVERTISEMENT
  • Zanga-zanga: Kotu Ta Bayar Da Belin Matasa 67 A Kan N670m
  • Matasa 5 Cikin Masu Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Sun yanke Jiki Sun Faɗi A Kotu

Wadannan bukukuwa za su kai kayayyakin Sin zuwa Afirka, kana a sa’i daya, wani bikin baje kolin da zai gudana a kasar Sin, a nasa bangare zai kai dimbin kayayyakin Afirka zuwa kasuwar kasar Sin. Daga ranar 5 zuwa ta 10 ga watan Nuwamba, za a gudanar da bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su cikin kasar Sin daga ketare wato CIIE karo na 7 a birnin Shanghai na kasar Sin, inda za a nuna dimbin kayayyakin da kasar Sin take shigowa da su daga ketare, ciki har da kasashen Afirka, musamman ma bisa yarjeniyoyin da kasashen Afirka suka kulla da kasar Sin a wajen taron dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka da ya gudana a bana, misali gyadar Najeriya, da ruwan zuman kasar Rwanda, da waken gahawa na kasar Burundi, gami da kifayen kasar Madagascar, da dai sauransu.

 

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Wadannan bukukuwan da za su gudana sun nuna yanayi mai armashi na cudanyar Sin da Afirka a fannin tattalin arziki da na ciniki, kana wani babban dalilin da ya sa ake samun wannan yanayi mai kyau shi ne karuwar tattalin arzikin Sin, duba da cewa a watanni 9 na farko na bana, cinikin da aka yi tsakanin kasar Sin da sauran kasashe da yankuna fiye da 160 ya karu sosai, kana saurin karuwar jamillar GDP ta Sin yana kan gaba a cikin manyan tattalin arzikin duniya. Karuwar tattalin arzikin Sin, da karin matakan da gwamnatin kasar ta dauka don sa kaimi ga ci gaban tattalin arziki, sun sa kungiyoyin hada-hadar kudi irinsu Goldman Sachs, da JPMorgan Chase, da Swiss Bank, dukkansu sun daga matsayin hasashen da suka yi dangane da karuwar tattalin arzikin Sin a bana.

 

Sai dai me ya sa karuwar tattalin arzikin Sin kan janyo ci gaban bangaren ciniki da tattalin arziki a kasashen Afirka? Dalili shi ne, kasar Sin ta dukufa wajen samar da damar raya tattalin arziki ga kasashe daban daban a yayin da take kokarin zamanantar da kanta, da kuma tabbatar da ci gaba na bai daya na daukacin kasashe masu tasowa. Wadannan matakai sun dace da manufar kasar ta gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkan bil Adam. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.