• English
  • Business News
Thursday, September 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Himmatu Wajen Rage Raɗaɗin Da ‘Yan Nijeriya Ke Ciki, In Ji Minista

by Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Tinubu Ya Himmatu Wajen Rage Raɗaɗin Da ‘Yan Nijeriya Ke Ciki, In Ji Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Shugaba Bola Tinubu ya ƙudiri aniyar rage raɗaɗin da ‘yan Nijeriya ke ciki.

 

Idris ya bayyana haka ne a ranar Lahadi a Kaduna a shirin ‘Hannu Da Yawa’ na Gidan Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN), Sashen Hausa.

  • An Bukaci Amurka Da Ta Inganta Hadin Gwiwa Da Kasar Sin Kan AI
  • Katsewar Wutar Lantarki: Mun Yi Asarar Fiye Da Naira Biliyan 6 – KEDCO 

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa ministan ya yi magana kan wahalar da aka samu sakamakon cire tallafin man fetur, kuma ya ce tallafin yana amfanar wasu tsirarun mutane ne kawai.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

Ya ba da tabbacin cewa tattalin arzikin ƙasar nan zai daidaita, kuma babu wata gwamnati da za ta so a samu ci-baya a zamanin ta.

 

Idris ya jaddada cewa abin da ya kamata a gyara a ƙasar nan ba ya ta’allaƙa ne ga Majalisar Dokoki ta Ƙasa, wakilai da aka zaɓa ko kuma masu zartaswa na gwamnati kawai ba ne, amma har ga duk ‘yan Nijeriya ne.

 

Ya yi nuni da cewa a kwanakin baya Tinubu ya umurci ministoci da su rage kuɗin gudanar da mulki ta hanyar taƙaita yawan motocin su a lokacin da suke gudanar da ayyukan su da kuma yawan ma’aikatan su a lokacin tafiye-tafiye.

 

Idris ya ce, “Shugaba Tinubu yana nuna buƙatar a sauya daga yadda ake tafiyar da al’amura a Nijeriya.

 

“A duk lokacin da muka zauna taron Majalisar Zartaswa ta Tarayya (FEC), abin da Shugaban Ƙasa ke jaddadawa shi ne buƙatar a rage kashe kuɗaɗe da yawa waɗanda ba su zama dole ba wajen gudanar da mulki.

 

“Shugaba Tinubu har ma ya ba da sanarwa kan kuɗin tafiya da yawan ababen hawa. Ana iya ganin wannan a matsayin abu ƙanƙani, amma a zahiri yana da muhimmanci.”

 

Ministan ya ce ta fuskar noma, Tinubu ya ce an canja wa Ma’aikatar Noma da Raya Karkara suna zuwa Ma’aikatar Noma Da Samar Da Abinci ta yadda za a magance matsalolin noma ta ɓangarori daban-daban.

 

Haka zalika ya bayyana cewa Tinubu na magance matsalolin rashin tsaro kai-tsaye, inda ya ƙara da cewa tun kafin zuwan gwamnatin sa ne ake fuskantar matsalolin.

 

Idris ya ƙara da cewa har yanzu Gwamnatin Tarayya tana kan hanyar samar da dandamali da kuma tabbatar da jin daɗin jami’an tsaro domin inganta tsarin tsaron ƙasa.

 

Ya ƙara da cewa har yanzu Shugaban Ƙasa na neman shawarwari kan ba samar da ‘yan sandan jihohi.

 

Da yake ƙarin bayani, Idris ya ce ɗauke wutar lantarki da aka yi a sassan arewacin ƙasar nan kwanan nan ba wani shiri ne aka yi ba kamar yadda wasu suke cewa.

 

Ya nanata cewa babu wani shugaba da zai so da gangan al’ummar sa su kasance cikin halin rashin wutar lantarki da sauran matsaloli.

 

Ministan ya ƙara da cewa, “Shugaban Ƙasa yana bakin ƙoƙarin sa wajen ganin an samar da dauwamammiyar mafita kan matsalar lalacewar wuta a ƙasar nan.

 

“Haka nan ana gab da kammala aikin bututun iskar gas na AKK wanda zai taimaka wajen inganta masana’antu a Arewa.”

 

Idris ya buƙaci jama’a da su riƙa amfani da kafafen sadarwa na zamani wajen yaɗa labaran ƙasar nan ta hanyar da ta dace, yana kokawa da yadda ake yaɗa labaran ƙarya.

 

Ministan, yayin da ya yarda cewa lamari ne da ya shafi duniya, ya buƙaci yin amfani da kafafen ta hanya mai kyau.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kuncin rayuwaTabarbarewar Tattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

CIIE Ya Tabbatar Da Matsayin Kasar Sin A Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

Me Ya Faru Gwamna Abba Yusuf Ya Daina Ɗaukar Wayar Kwankwaso?

Related

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

1 hour ago
Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano
Labarai

Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

2 hours ago
Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 
Manyan Labarai

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

2 hours ago
Hatsarin Jiragen Ruwa
Labarai

Mutane 29 Sun Rasa Rayukansu A Wani Hatsarin Jirgin Ruwa A Jihar Neja

5 hours ago
Shettima
Labarai

Za Mu Kare Bukatun Nijeriya A Mashigin Tekun Guinea – Shettima

5 hours ago
Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 
Manyan Labarai

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

7 hours ago
Next Post
Me Ya Faru Gwamna Abba Yusuf Ya Daina Ɗaukar Wayar Kwankwaso?

Me Ya Faru Gwamna Abba Yusuf Ya Daina Ɗaukar Wayar Kwankwaso?

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

September 3, 2025
Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

September 3, 2025
Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

September 3, 2025
Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

September 3, 2025
Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

September 3, 2025
Lookman

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

September 3, 2025
Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

September 3, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Mutane 29 Sun Rasa Rayukansu A Wani Hatsarin Jirgin Ruwa A Jihar Neja

September 3, 2025
Shettima

Za Mu Kare Bukatun Nijeriya A Mashigin Tekun Guinea – Shettima

September 3, 2025
Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

September 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.