ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
Sin

Yayin da tutoci suka rika kadawa, kade-kade na tsuma maza suka rika tashi, kusan ko ina ya cika da batun tarihi a titunan birnin Beijing, ba sai an fada ba sakon ya fito fili karara, wato jama’ar kasar Sin na tunawa da samun nasararsu a kan kare martabar kasa daga zaluncin mamayar dakarun Japanawa.

Yau Laraba, 3 ga watan Satumba, rana ce ta cika shekaru 80 da samun wani muhimmin lokaci a tarihin zamani da ya kunshi manyan abubuwa biyu, na farko nasarar jama’ar kasar Sin a kan zaluncin Japanawa, da kuma babbar nasarar da sojojin kawance suka samu a yaki da mulkin danniya a duniya wanda aka fi sani da Yakin Duniya Na Biyu.

  • Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 
  • NAFDAC Ta Gano Wasu Jabun Allurai A Kasuwanni, Ta Gargaɗi Jama’a Kan Amfani Da Su

Gagarumin bikin ranar da aka yi yau a kasar Sin ba wai kawai na tunawa da nasarar soja ba ne, girmamawa ce ga tsayin daka, sadaukarwa, da hadin kan al’ummar da ta yi fama da tashe-tashen hankula na tsawon shekaru 14. Tun daga abin da ya faru a ranar 18 ga Satumba a shekarar 1931 (na kaddamar da hare-hare) zuwa mika wuyar kasar Japan a shekarar 1945, kasar Sin ta yi gwagwarmayar tsira da mutuncinta daga mamayar zalunci har ta kai ga asarar rayukan sojoji da fararen hula fiye da miliyan 35. Kuma duk da shiga cikin tsananin wahalhalu da ba za a iya misaltawa ba, jama’ar kasar Sin sun tsaya tsayin daka, tare da ba da gudummawa sosai ga fatattakar ‘yan mulkin danniya a duniya.

ADVERTISEMENT

Gadon tsayin dakar da jama’ar kasar Sin suka yi shi ne ya zama ruhin kasar, ya kuma ba da gudunmawa ga haifar da sabon tsari na duniya a karkashin Majalisar Dinkin Duniya, tare da sadaukar da kai ga zaman lafiya a tsakanin al’ummomin duniya. Sai dai kuma, a yayin da tashe-tashen hankula a duniya ke kara ta’azzara a zamanin nan kuma masu ba da labarin abin da ya faru suka fara gurbata hakikanin tarihi, rawar da kasar Sin ke takawa wajen kare gaskiyar lamarin na da matukar muhimmanci.

Jawabin da shugaba Xi Jinping ya yi a taron Tianjin na Kungiyar Hadin Gwiwar Shanghai (SCO), ya sake jaddada aniyar kasar Sin wajen raya mu’amala da bangarori daban daban, da daidaiton ‘yancin kasashe, da hadin gwiwar duniya baki daya. Gabatar da shawarar Tsarin Shugabancin Duniya (GGI) ta nuna sabon kokari na kiyaye kyawawan ka’idojin da aka kafa bayan yakin duniya na biyu domin ci gaban kasa da kasa.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Kazalika, wannan biki na tunawa da nasarar fatattakar zalunci yana tunatar da mu mahimmancin waiwaye a kan tarihi. Fina-finai da aka yi game da hakan kamar “Dead to Rights”, da bikin nune-nunen a sassan yankin Macao, da faretin soja a birnin Beijing, hidindimu ne na sake duba tarihi, da sadaukarwar al’ummomin da suka gabata domin ci gaba da zaburar da na yanzu da wadanda za su zo gaba.

Birnin Beijing ya cika da annashuwa da alfahari yayin da dandalin Tian’anmen ya shaida gagarumin faretin soji domin bikin na yau. An yi gaisuwar ban-girma ta hanyar harba bindigogi 80 a sassan babban birnin domin karrama mazan jiya da suka kwanta dama da kuma wadanda suke raye. Sojoji sun yi tattaki cikin tsari mai kyau, jiragen sama sun yi fenti mai launin ja da zinariya a sararin sama, kuma tsoffin sojoji da suka halarci bikin sun kasance a matsayin shaida na jajircewa.

Shagulgulan al’adu da shirye-shiryen gidajen rediyo da talabijin da aka watsa a sassan kasar har ma da duniya baki daya sun kara raya ruhin tunawa da wannan nasara a cikin gidaje da zukatan jama’a a fadin kasar da sauran abokai na kasa da kasa. Yanayin yau a kasar Sin ya kasance na biki mai matukar armashi da ke kara girman kishin kasa tare da girmamawa ga sadaukarwar da aka yi shekaru 80 da suka gabata.

Darussan wannan tarihi a bayyane suke, wato hadin kai wajen fuskantar zalunci da kuma kiyaye mutunci domin tabbatar da adalci a doron kasa kuma tabbas, kasar Sin ta nuna gado mai kyau ta wannan fuska. Don haka, ya kamata wannan rana ta zama ba lokacin tunani ne kawai a kan nasarar da aka samu ba, amma a kan abin da ya zama wajibi a kiyaye shi. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Shettima

Za Mu Kare Bukatun Nijeriya A Mashigin Tekun Guinea - Shettima

LABARAI MASU NASABA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.