• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sake Gina Aminci Tsakanin Sin Da Amurka Zai Amfani Duniya Baki Daya

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sake Gina Aminci Tsakanin Sin Da Amurka Zai Amfani Duniya Baki Daya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A shekarun baya bayan nan, ana ta ganin karuwar sabani, da rashin daidaito ta fuskar alakar Sin da Amurka, wanda hakan ke da matukar hadari ga dunkulewar duniya da cimma nasara tare.

 

A halin yanzu, yanayin alakar kasashen biyu na cike da kalubale, ya kuma gaza hawa turba mai inganci da za ta haifar da moriya ga sassa biyu da ma duniya baki daya. Hakan ya sa masharhanta ke ganin lokaci ya yi manyan kasashen biyu mafiya karfin tattalin arziki a duniya, za su rungumi hanyoyin da ba na fito na fito ba, wajen shawo kan mummunar takara, su kuma amince da tafarki guda na cimma nasara wadda kowa zai ci gajiyarta.

  • Xi Ya Taya Trump Murnar Lashe Zaben Shugaban Amurka
  • Sin Ta Yi Alkawarin Fadada Bude Kofa Da Hadin Gwiwa Da Kasa Da Kasa

A ganina, hanya daya tilo ta kaiwa ga cimma wannan nasara ita ce dukkanin sassan biyu su amine cewa za su iya bin hanyoyin cimma daidaito cikin lumana, da tattaunawa, wadanda za su dace da zaman jituwa da moriyarsu.

 

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Yayin da Sin da Amurka ke kara fadada tasirinsu ta hanyar karfafa alaka da sauran sassan duniya, fifikon Amurka shi ne karfin ikon ayyukan soji, da samar da kariyar tsaro ga kawayenta da tasiri a siyasar duniya. A hannu guda kuwa, kasar Sin na mayar da hankali ne ga fadada zaman jituwa, da zuba jari, da ingiza cinikayya tsakaninta da sauran kasuwannin duniya.

 

Kafin shekarar 2001, wato shekarar da kasar Sin ta shiga kungiyar cinikayya ta duniya ko WTO, kaso 80 bisa dari na kasashen duniya suna gudanar da hada-hadar cinikayya ne da Amurka sama da yadda suke yi da kasar Sin. Amma a yau, manufofin kasar Sin irin su shawarar nan ta “Ziri daya da hanya daya, sun haifar da fadadar cinikayya tsakanin Sin da kasashen duniya 128 cikin 190 sama da yadda suke yi da Amurka.

 

Nan gaba kadan za a kafa sabuwar gwamnatin Amurka, kuma fatan al’ummun duniya shi ne wannan sabuwar gwamnati ta zo da tsarin sassanta alaka da Sin, ta yadda hadin gwiwarsu za ta ingiza daidaito, da ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya. Kana duniya ta ci gajiya daga nasarar da kyautatuwar alakar manyan kasashen biyu za ta haifar. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sabuwar Ƙungiya Ƴan Ta’adda Ta Ɓulla A Sokoto – Shalƙwatar Tsaro 

Next Post

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 481, Sun Kama Wasu 741, Sun Ceto Mutane 492 A Watan Oktoba

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

7 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

8 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

9 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

10 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

12 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

1 day ago
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 481, Sun Kama Wasu 741, Sun Ceto Mutane 492 A Watan Oktoba

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 481, Sun Kama Wasu 741, Sun Ceto Mutane 492 A Watan Oktoba

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.