• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Garkuwa Da Sama Da ‘Yan Nijeriya 971 A Watan Oktoban 2024 – Rahoto

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
7 months ago
in Labarai
0
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani rahoto ya bayyana cewa ‘yan Nijeriya sama da 971 aka yi garkuwa da su a sassa daban-daban na kasar a watan Oktoban 2024.

 

Wannan fallasa na zuwa ne a daidai lokacin da wata sabuwar kungiyar ta’addanci ta kunno kai mai suna ‘Lakurawa’ a yankin arewa maso yammacin kasar.

  • A Karon Farko Adadin Motoci Masu Aiki Da Sabon Makamashi Da Kasar Sin Ke Kerawa Duk Shekara Ya Zarce Miliyan 10
  • Kawu Sumaila Ya Yi Barazanar Maka Shugaban NNPP Na Kano A Kotu

Bayanan na kunshe ne a cikin rahoton tsaron Nijeriya na Oktoban 2024, wanda wani kamfani mai kula da hadarin tsaro da kuma kamfanin tuntubar bayanan sirri suka gabatar a ranar Talata.

 

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Rahoton ya ce ana samun tabarbarewar matakan tsaro na al’amura da suka hada da garkuwa da mutane da kuma asarar rayuka a kasar nan, yana mai gargadin cewa karuwar adadin ya nuna cewa shekarar 2024 za ta kasance shekara mafi muni a ayyukan rashin tsaro cikin shekaru goma.

 

Ya yi bayanin cewa watan da ake bitar an gudanar da shi ne ta amfani da al’amuran da ke da alaka da tashe-tashen hankula, da suka hada da kashe-kashe da yin garkuwa da mutane domin neman kudin fansa musamman daga kungiyoyi masu aikata laifuka, kungiyoyin asiri, da kungiyoyin sa kai na kabilanci, da tashe-tashen hankula a cikin al’umma.

 

Kamfanin tsaron ya bayyana cewa, bayanan da aka tattara sun nuna cewa kasar ta samu karuwar mace-mace da kashi 51 da kuma karuwar satar mutane da kashi 24.42.

 

Binciken ya nuna cewa Nijeriya ta samu matsalar tsaro 861, inda kashi 64.92 aka alakanta su da barazanar tsaro, kashi 24.79 sun kunshi ayyukan jami’an tsaro, sannan 4.99 an danganta su da tsaron abubuwan da suka faru daga Oktoban 2024.

 

A cikin watan da aka yi bitar, kasar ta kuma sami asarar rayuka 1545, inda kashi 67.70 ke da nasaba da mutuwar fararen hula, kashi 25.89 ga masu aikata laifuka, sannan kashi 6.40 kuma an danganta su ga jami’an tsaro da kuma mutane 971 da aka sace.

 

Dangane rahoton a sassan fadin kasar nan, yankunan arewa maso gabas da arewa maso yamma ne suka fi fama da matsalar tsaro, wanda ya kai kashi 52.03 na al’amuran da suka faru, yayin da yankin kudu maso gabas ya bayar da rahoton mafi karancin abubuwan da suka faru a kashi 7.78.

 

Haka kuma binciken nuna cewa adadin mutanen da aka kashe ya karu daga 1,022 a watan Satumba na 2024 zuwa 1,545 a watan Oktoban 2024, wanda ke nuna karuwar kashi 51.17.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bankin Duniya Da Hukumar Lamuni Ke Yi Wa Tsarin Ilimin Nijeriya Zagon-kasa – ASUU

Next Post

Binciken CGTN Ya Nuna Amincewa Da Kokarin Kasar Sin Dangane Da Aiwatar Da Matakan Dakile Sauyin Yanayi

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

4 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

5 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

6 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

10 hours ago
Garkuwa
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

11 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

12 hours ago
Next Post
Binciken CGTN Ya Nuna Amincewa Da Kokarin Kasar Sin Dangane Da Aiwatar Da Matakan Dakile Sauyin Yanayi

Binciken CGTN Ya Nuna Amincewa Da Kokarin Kasar Sin Dangane Da Aiwatar Da Matakan Dakile Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.