ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Garkuwa Da Sama Da ‘Yan Nijeriya 971 A Watan Oktoban 2024 – Rahoto

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 years ago
Garkuwa

Wani rahoto ya bayyana cewa ‘yan Nijeriya sama da 971 aka yi garkuwa da su a sassa daban-daban na kasar a watan Oktoban 2024.

 

Wannan fallasa na zuwa ne a daidai lokacin da wata sabuwar kungiyar ta’addanci ta kunno kai mai suna ‘Lakurawa’ a yankin arewa maso yammacin kasar.

ADVERTISEMENT
  • A Karon Farko Adadin Motoci Masu Aiki Da Sabon Makamashi Da Kasar Sin Ke Kerawa Duk Shekara Ya Zarce Miliyan 10
  • Kawu Sumaila Ya Yi Barazanar Maka Shugaban NNPP Na Kano A Kotu

Bayanan na kunshe ne a cikin rahoton tsaron Nijeriya na Oktoban 2024, wanda wani kamfani mai kula da hadarin tsaro da kuma kamfanin tuntubar bayanan sirri suka gabatar a ranar Talata.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Rahoton ya ce ana samun tabarbarewar matakan tsaro na al’amura da suka hada da garkuwa da mutane da kuma asarar rayuka a kasar nan, yana mai gargadin cewa karuwar adadin ya nuna cewa shekarar 2024 za ta kasance shekara mafi muni a ayyukan rashin tsaro cikin shekaru goma.

 

Ya yi bayanin cewa watan da ake bitar an gudanar da shi ne ta amfani da al’amuran da ke da alaka da tashe-tashen hankula, da suka hada da kashe-kashe da yin garkuwa da mutane domin neman kudin fansa musamman daga kungiyoyi masu aikata laifuka, kungiyoyin asiri, da kungiyoyin sa kai na kabilanci, da tashe-tashen hankula a cikin al’umma.

 

Kamfanin tsaron ya bayyana cewa, bayanan da aka tattara sun nuna cewa kasar ta samu karuwar mace-mace da kashi 51 da kuma karuwar satar mutane da kashi 24.42.

 

Binciken ya nuna cewa Nijeriya ta samu matsalar tsaro 861, inda kashi 64.92 aka alakanta su da barazanar tsaro, kashi 24.79 sun kunshi ayyukan jami’an tsaro, sannan 4.99 an danganta su da tsaron abubuwan da suka faru daga Oktoban 2024.

 

A cikin watan da aka yi bitar, kasar ta kuma sami asarar rayuka 1545, inda kashi 67.70 ke da nasaba da mutuwar fararen hula, kashi 25.89 ga masu aikata laifuka, sannan kashi 6.40 kuma an danganta su ga jami’an tsaro da kuma mutane 971 da aka sace.

 

Dangane rahoton a sassan fadin kasar nan, yankunan arewa maso gabas da arewa maso yamma ne suka fi fama da matsalar tsaro, wanda ya kai kashi 52.03 na al’amuran da suka faru, yayin da yankin kudu maso gabas ya bayar da rahoton mafi karancin abubuwan da suka faru a kashi 7.78.

 

Haka kuma binciken nuna cewa adadin mutanen da aka kashe ya karu daga 1,022 a watan Satumba na 2024 zuwa 1,545 a watan Oktoban 2024, wanda ke nuna karuwar kashi 51.17.

Garkuwa
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Garkuwa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
Binciken CGTN Ya Nuna Amincewa Da Kokarin Kasar Sin Dangane Da Aiwatar Da Matakan Dakile Sauyin Yanayi

Binciken CGTN Ya Nuna Amincewa Da Kokarin Kasar Sin Dangane Da Aiwatar Da Matakan Dakile Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.