• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Aikin Gina Tashar Mota Ta Zamani A Gusau

by Sulaiman
8 months ago
in Manyan Labarai
0
Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Aikin Gina Tashar Mota Ta Zamani A Gusau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na samar da guraben ayyukan yi ga mutanen da rayuwarsu ta dogara ga harkokin tashar mota.

 

A ranar Litinin ne gwamnan ya ƙaddamar da aikin gina tashar mota ta zamani a kan titin Sakkwato zuwa Zariya a Gusau, babban birnin jihar.

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Rungumi Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa
  • Babu Wata Kasa Da Za Ta Ce ”Ita Kadai Ta Isa Gayya”

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa, aikin da aka bai wa kamfanin Fieldmark Construction zai haɗa da isassun wuraren ajiye motoci, wuraren hutawa na direbobi, ingantattun na’urorin tsaro, da tsarin bayar da tikitin shiga mota don komai ya zama cikin tsari.

 

Labarai Masu Nasaba

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

A jawabinsa a wajen ƙaddamar da aikin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada cewa aikin wani muhimmin bangare ne na ƙudirin gwamnatinsa na inganta ababen more rayuwa a yankunan Gusau.

 

Ya ƙara da cewa, “Wannan shiri zai inganta tsaro, da inganta samar da kuɗaɗen shiga, da kuma bai wa jiharmu damar yin gogayya da sauran jihohi a faɗin ƙasar nan.

 

“Wannan katafaren tashar motoci ta zamani za ta ƙunshi kayayyakin zamani da aka tsara domin ɗaukar masu ababen hawa na haya da fasinjoji cikin aminci, inganci da tsari.

 

“Sauran muhimman abubuwan da ke cikin wannan aikin sun haɗa da wuraren ajiye motoci da za su nufi kowace jiha, ofishin ‘yan sanda, asibiti, tashar kashe gobara, masallaci, ofishin shuganannin tasha, ofishin ƙungiyar ’yan mota, ban ɗakuna, otel ɗin tasha, wurin lodi, kantin sayar da kayayyaki, wurin zubar da shara, rumbun ajiya, garejin gyaran mota da wurin wankin mota.

 

“A yayin gudanar da aikin, aikin zai ɗauki ƙwararrun ma’aikata da marasa ƙwarewa, kuma da zarar an fara aiki, wurin zai zama cibiyar hada-hadar kasuwanci, wanda zai amfanar da ‘yan kasuwa da masu sauran ayyuka.

 

Gwamnan ya sake tabbatar da cewa samar da muhimman ababen more rayuwa, kamar hanyoyin da gwamnatinsa ta fara ginawa jim kaɗan bayan hawansa mulki – wasu daga cikinsu an ƙaddamar da su ne a yayin bikin cika shekara ɗaya – yana ɗaya daga cikin mafi inganci hanyoyin bunƙasa harkokin kasuwanci da samar wadata a jihar.

 

“Bayan tasirinsa na habaka tattalin arziki, wannan shiri wata hanya ce ta ƙawata babban birnin jiharmu ta hanyar hangen nesa mai zurfi na samar da yanayi na zamani kuma mai inganci ga rayuwar jama’armu.

 

“Da waɗannan kalamai, ina farin cikin ƙaddamar da aikin gina sabuwar tashar mota ta Gusau a hukumance. Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya sanya albarka a wannan aiki, ya kuma sa ya zama silar wadata da ci gaba ga al’ummar Jihar Zamfara.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Arewa Maso Yammasiyasar NijeriyaTa'addanci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Biodun Ya Amince Da ₦70,000 Mafi Ƙarancin Albashi Ga Ma’aikatan Ekiti

Next Post

Zargin Tarayya Da Matar Aure: Miji Ya Ki Amincewa Da Hukuncin Kotun Da Ta Wanke Kwamishinan Jigawa

Related

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

6 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

22 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

1 day ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

1 day ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

2 days ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

2 days ago
Next Post
Zargin Tarayya Da Matar Aure: Miji Ya Ki Amincewa Da Hukuncin Kotun Da Ta Wanke Kwamishinan Jigawa

Zargin Tarayya Da Matar Aure: Miji Ya Ki Amincewa Da Hukuncin Kotun Da Ta Wanke Kwamishinan Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.