• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Aikin Gina Tashar Mota Ta Zamani A Gusau

bySulaiman
11 months ago
Gwamna Lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na samar da guraben ayyukan yi ga mutanen da rayuwarsu ta dogara ga harkokin tashar mota.

 

A ranar Litinin ne gwamnan ya ƙaddamar da aikin gina tashar mota ta zamani a kan titin Sakkwato zuwa Zariya a Gusau, babban birnin jihar.

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Rungumi Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa
  • Babu Wata Kasa Da Za Ta Ce ”Ita Kadai Ta Isa Gayya”

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa, aikin da aka bai wa kamfanin Fieldmark Construction zai haɗa da isassun wuraren ajiye motoci, wuraren hutawa na direbobi, ingantattun na’urorin tsaro, da tsarin bayar da tikitin shiga mota don komai ya zama cikin tsari.

 

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

A jawabinsa a wajen ƙaddamar da aikin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada cewa aikin wani muhimmin bangare ne na ƙudirin gwamnatinsa na inganta ababen more rayuwa a yankunan Gusau.

 

Ya ƙara da cewa, “Wannan shiri zai inganta tsaro, da inganta samar da kuɗaɗen shiga, da kuma bai wa jiharmu damar yin gogayya da sauran jihohi a faɗin ƙasar nan.

 

“Wannan katafaren tashar motoci ta zamani za ta ƙunshi kayayyakin zamani da aka tsara domin ɗaukar masu ababen hawa na haya da fasinjoji cikin aminci, inganci da tsari.

 

“Sauran muhimman abubuwan da ke cikin wannan aikin sun haɗa da wuraren ajiye motoci da za su nufi kowace jiha, ofishin ‘yan sanda, asibiti, tashar kashe gobara, masallaci, ofishin shuganannin tasha, ofishin ƙungiyar ’yan mota, ban ɗakuna, otel ɗin tasha, wurin lodi, kantin sayar da kayayyaki, wurin zubar da shara, rumbun ajiya, garejin gyaran mota da wurin wankin mota.

 

“A yayin gudanar da aikin, aikin zai ɗauki ƙwararrun ma’aikata da marasa ƙwarewa, kuma da zarar an fara aiki, wurin zai zama cibiyar hada-hadar kasuwanci, wanda zai amfanar da ‘yan kasuwa da masu sauran ayyuka.

 

Gwamnan ya sake tabbatar da cewa samar da muhimman ababen more rayuwa, kamar hanyoyin da gwamnatinsa ta fara ginawa jim kaɗan bayan hawansa mulki – wasu daga cikinsu an ƙaddamar da su ne a yayin bikin cika shekara ɗaya – yana ɗaya daga cikin mafi inganci hanyoyin bunƙasa harkokin kasuwanci da samar wadata a jihar.

 

“Bayan tasirinsa na habaka tattalin arziki, wannan shiri wata hanya ce ta ƙawata babban birnin jiharmu ta hanyar hangen nesa mai zurfi na samar da yanayi na zamani kuma mai inganci ga rayuwar jama’armu.

 

“Da waɗannan kalamai, ina farin cikin ƙaddamar da aikin gina sabuwar tashar mota ta Gusau a hukumance. Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya sanya albarka a wannan aiki, ya kuma sa ya zama silar wadata da ci gaba ga al’ummar Jihar Zamfara.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Next Post
Zargin Tarayya Da Matar Aure: Miji Ya Ki Amincewa Da Hukuncin Kotun Da Ta Wanke Kwamishinan Jigawa

Zargin Tarayya Da Matar Aure: Miji Ya Ki Amincewa Da Hukuncin Kotun Da Ta Wanke Kwamishinan Jigawa

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version