• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wata Kasa Da Za Ta Ce ”Ita Kadai Ta Isa Gayya”

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Babu Wata Kasa Da Za Ta Ce ”Ita Kadai Ta Isa Gayya”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An yi zama na II na taron kungiyar G20 karo na 19 a jiya Litinin, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da jawabi mai taken ”Hada Hannu Domin Tafiyar da Tsarin Tattalin Arzikin Duniya Bisa Adalci da Daidaito”. 

 

A ra’ayina, wannan jawabi ya gabatar da shawarwari da hanya mai sauki ta shawo kan matsalolin tattalin arziki da duniya ke fama da su, har ma da hanyoyin da kasashe za su iya hada hannu domin taimakon juna.

  • Sin Da Afirka Na Da Buri Daya A Wajen Taron G20
  • Shugaba Xi Jinping Ya Ce Kasar Sin Da Birtaniya Na Da Dimbin Sararin Yin Hadin Gwiwa

Daga cikin kalaman shugaba Xi, akwai wadanda suka fi jan hankalina, inda yake cewa, ya kamata a yi adawa da kariyar cinikayya da ra’ayin bangare daya da sanya yarjejeniyar saukaka zuba jari domin samun ci gaba, cikin tsarin dokokin WTO.

 

Labarai Masu Nasaba

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Zan iya cewa, cikin wadannan kalamai kalilan, shugaban ya gabatar da mafita mafi sauki ga matsalolin duniya. Idan muka dauki batun kariyar cinikayya da zartar da ra’ayin bangare guda da wasu kasashen duniya ke ganin su ne mafita gare su, mun riga mun ga yadda hakan bai amfanawa kowannne bangare da komai ba. Ci gaban wata kasa, dama ce ga sauran kasashen duniya maimakon barazana ko kalubale. Mun riga mun gane cewa, babu wata kasa da za ta iya cewa za ta raba gari da wata, domin makomar kasashen na hade da juna. Idan wata na fama da talauci ko matsaloli, to wadannan matsaloli na iya bazuwa ga sauran, haka ma idan tana cikin wadata da kwanciyar hankali. Idan muka dauki Sin a matsayin misali, muhimmiyar rawar da take takawa wajen samarwa duniya damarmaki da dimbin gudunmuwarta ga ci gaban tattalin arzikin duniya, abu ne da ba zai misaltu ba, don haka, babu wata kasa da za ta ce ta yanke mu’amala da ita ko kuma ta bugi kirjin cewa ita kadai (kasar) ta isa gayya.

 

Idan har ba neman fifiko ko mulkin danniya ba, to mene ne dalilin wariya ko kariyar cinikayya tsakanin kasashe bayan mafita ita ce hada hannu tsakaninsu domin cin moriyar juna? A wannan zamani da ake ciki, ba zai yuwu duniya ta ci gaba da kasancewa karkashin ikon wata kasa daya ko wasu kasashe kalilan ba, dole ne irin wadannan kasashe su zubar da girman kai su hada kai da sauran takwarorinsu domin ceto duniya daga fadawa mummunan yanayi. (Fa’iza Musatapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Da Afirka Na Da Buri Daya A Wajen Taron G20

Next Post

Kwalara Ta Yi Ajalin Mutane 25 A Sakkwato

Related

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika
Daga Birnin Sin

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

11 hours ago
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

12 hours ago
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

13 hours ago
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya
Daga Birnin Sin

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

14 hours ago
An Sanya Kaburburan Sarakunan Daular Xixia Ta Kasar Sin Cikin Muhimman Wuraren Tarihi Na UNESCO
Daga Birnin Sin

An Sanya Kaburburan Sarakunan Daular Xixia Ta Kasar Sin Cikin Muhimman Wuraren Tarihi Na UNESCO

16 hours ago
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

1 day ago
Next Post
Kwalara Ta Yi Ajalin Mutane 25 A Sakkwato

Kwalara Ta Yi Ajalin Mutane 25 A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

July 13, 2025
Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

July 13, 2025
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.