• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Shugabannin Kasashen Faransa Da Jamus Da Argentina A Gefen Taron Kolin G20

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Shugabannin Kasashen Faransa Da Jamus Da Argentina A Gefen Taron Kolin G20
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Talata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron, da shugaban gwamnatin kasar Jamus Olaf Scholz, da kuma shugaban kasar Argentina Javier Milei a gefen taron kolin kungiyar G20 a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil. 

 

Yayin ganawarsa da shugaban kasar Faransa, Xi ya ce, Sin da Faransa manyan kasashe ne dake da cikakken ‘yancin kai dake sauke nauyin dake wuyansu, huldarsu na da babbar daraja a bangaren manyan tsare-tsare da babbar ma’ana a duk fadin duniya. Ya kamata, bangarorin biyu su zurfafa cudanya ta fuskar manyan tsare-tsare da kara goyawa juna baya, ta yadda za a tabbatar da bunkasuwar huldar kasashen biyu mai dorewa da yakini, don taka rawar gani kan raya huldar Sin da Turai yadda ya kamata da zaman lafiya da kwanciyar hankalin duniya.

  • Pep Guardiola Ya Tsawaita Kwantiragi A Manchester City Har Zuwa Shekarar 2027
  • Sin Tana Fatan Raya Duniya Mai Adalci Dake Samun Bunkasuwa Tare Tsakanin Mabambantan Bangarori

Haka kuma, a yayin ganawarsa da shugaban gwamnatin kasar Jamus, Xi Jinping ya bayyana cewa, akwai bukatar kasashen Sin da Jamus su duba da raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu na dogon lokaci bisa manyan tsare-tsare. Ya bayyana cewa, bangarorin biyu sun yi tattaunawa ta gaskiya, mai zurfi da kyakkyawar sakamako yayin ziyarar da Scholz ya kawo kasar Sin a watan Afrilu. Yana mai cewa, a cikin watannin da suka gabata, hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu ya samu sakamako mai ma’ana a fannonin samun bunkasuwa ba tare da gurbata muhalli ba, da sufuri mai dorewa, da hadin gwiwar raya aikin gona a Afirka, yayin da dangantakar dake tsakanin kasashen biyu ke ci gaba da nuna sabon karfi da kuzari.

 

Labarai Masu Nasaba

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Bugu da kari, a yayin ganawarsa da shugaban kasar Argentina, Kasashen Sin da Argentina sun yi alkawarin ba da goyon baya wajen inganta raya shawarar “Ziri daya da hanya daya”. Da yake karin haske game da makomar hadin gwiwar da za a yi gaba, Xi ya ce, tsarin tattalin arziki da cinikayya na kasashen Sin da Argentina sun yi matukar dacewa da juna, yana mai bayyana fatan bangarorin biyu za su iya fadada hadin gwiwa a fannonin makamashi, da samar da ababen more rayuwa na ma’adinai, da aikin gona, da kimiyya da fasaha, da tattalin arziki na dijital. (Mai Fassara: Amina Xu, Mohammed Baba Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kama Dillalin Safarar Makamai Dan Aljeria A Zamfara 

Next Post

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Babban Taron Intanet Na Duniya Na Bana A Wuzhen

Related

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

3 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

5 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

5 hours ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

22 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

22 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

1 day ago
Next Post
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Babban Taron Intanet Na Duniya Na Bana A Wuzhen

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Babban Taron Intanet Na Duniya Na Bana A Wuzhen

LABARAI MASU NASABA

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Sin

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.