• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kujerar Ɗindindin A Majalisar Dinkin Duniya: Tinubu Na Kamun Ƙafa Wurin Shugabannin G20

byYusuf Shuaibu
11 months ago
Duniya

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu ya ce akwai bukatar kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya yi garambawul a tsarinsa domin tabbatar da ci gaba da dacewarsa a harkokin duniya.

Shugaban, wanda ya nanata shirye-shiryen da NIjeriya ke da ita na wakiltar Afirka a cikin Majalisar Dinkin Duniya, ya yi kira ga shugabannin kungiyar G20 da su amince Nahiyar Afirka ta samu kujeran dindindin a Majalisar Dinkin Duniya.

  • Tsarabar Taron Kolin G20
  • Jami’in Yada Labarai: Kasar Sin A Shirye Take Ta Aiwatar Da Hadin Gwiwar Kasashe Na Hakika Tare Da Mambobin G20

Ya yi wannan rokon ne a taron koli na shugabannin kungiyar G20 karo na 19 a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil.

Shugaba Tinubu ya ce, “Ya kamata kwamitin tsaro ya fadada rukunin mambobi na dindindin da wadanda ba na dindindin ba don nuna bambance-bambancen duniya da yawan jama’a, domin Afirka ta cancanci a ba ta kujeran dindindin a Majalisar Dinkin Duniya.

“Afirka ta cancanci fifiko a wannan tsari, kuma ya kamata a ba ta kujeru biyu na dindindin tare da daidaita matsayinta. A sherye Nijeriya take ta zama wakiliyar Afirka a wannan matsayi.”

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Sanarwar ta shugaban wadda Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yusuf Tuggar ya karanta a madadinsa, ta yi nuni da cewa, kungiyar G20 a halin yanzu tana sanye da wani tsari na cibiyoyi na kasa da kasa masu sa ido da ke goyon bayan ra’ayin sauye-sauye a bangarori da yawa.

Ya kuma yaba wa matakin da G20 ta dauka na bai wa kungiyar tarayyar Afirka damar zama mamba ta dindindin da kuma yadda take gayyatar kasashen da za su shiga kungiyar.

Shugaba Tinubu ya kuma yaba da kafa kungiyar kawance na yaki da yunwa da kuma fatara, wanda Shugaban kasar Brazil, Luiz Lula da Silba ke jagoranta, yana mai cewa kawancen na da matukar muhimmanci wajen yaki da yunwa da fatara a duniya.

Sannan ya yaba da shirin tare da bayyana shi a matsayin matakin da ya dace don magance daya daga cikin manyan kalubalen duniya.

Shugaba Tinubu ya kwatanta wannan shiri na duniya da daya daga cikin fannoni takwas da ya zayyana a bikin rantsar da shi watanni 18 da suka gabata, inda ya bayyana aniyar Nijeriya na daukar kyawawan halaye na kasa da kasa don ciyar da tattalin arzikinta gaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Next Post
Rayuwar Annabi Muhammadu (SAW) Da Abin Da Ya Ta’allaka Da Aurensa (2)

Rayuwar Annabi Muhammadu (SAW) Da Abin Da Ya Ta’allaka Da Aurensa (2)

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version