ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kujerar Ɗindindin A Majalisar Dinkin Duniya: Tinubu Na Kamun Ƙafa Wurin Shugabannin G20

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Duniya

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu ya ce akwai bukatar kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya yi garambawul a tsarinsa domin tabbatar da ci gaba da dacewarsa a harkokin duniya.

Shugaban, wanda ya nanata shirye-shiryen da NIjeriya ke da ita na wakiltar Afirka a cikin Majalisar Dinkin Duniya, ya yi kira ga shugabannin kungiyar G20 da su amince Nahiyar Afirka ta samu kujeran dindindin a Majalisar Dinkin Duniya.

  • Tsarabar Taron Kolin G20
  • Jami’in Yada Labarai: Kasar Sin A Shirye Take Ta Aiwatar Da Hadin Gwiwar Kasashe Na Hakika Tare Da Mambobin G20

Ya yi wannan rokon ne a taron koli na shugabannin kungiyar G20 karo na 19 a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil.

ADVERTISEMENT

Shugaba Tinubu ya ce, “Ya kamata kwamitin tsaro ya fadada rukunin mambobi na dindindin da wadanda ba na dindindin ba don nuna bambance-bambancen duniya da yawan jama’a, domin Afirka ta cancanci a ba ta kujeran dindindin a Majalisar Dinkin Duniya.

“Afirka ta cancanci fifiko a wannan tsari, kuma ya kamata a ba ta kujeru biyu na dindindin tare da daidaita matsayinta. A sherye Nijeriya take ta zama wakiliyar Afirka a wannan matsayi.”

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima

Sanarwar ta shugaban wadda Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yusuf Tuggar ya karanta a madadinsa, ta yi nuni da cewa, kungiyar G20 a halin yanzu tana sanye da wani tsari na cibiyoyi na kasa da kasa masu sa ido da ke goyon bayan ra’ayin sauye-sauye a bangarori da yawa.

Ya kuma yaba wa matakin da G20 ta dauka na bai wa kungiyar tarayyar Afirka damar zama mamba ta dindindin da kuma yadda take gayyatar kasashen da za su shiga kungiyar.

Shugaba Tinubu ya kuma yaba da kafa kungiyar kawance na yaki da yunwa da kuma fatara, wanda Shugaban kasar Brazil, Luiz Lula da Silba ke jagoranta, yana mai cewa kawancen na da matukar muhimmanci wajen yaki da yunwa da fatara a duniya.

Sannan ya yaba da shirin tare da bayyana shi a matsayin matakin da ya dace don magance daya daga cikin manyan kalubalen duniya.

Shugaba Tinubu ya kwatanta wannan shiri na duniya da daya daga cikin fannoni takwas da ya zayyana a bikin rantsar da shi watanni 18 da suka gabata, inda ya bayyana aniyar Nijeriya na daukar kyawawan halaye na kasa da kasa don ciyar da tattalin arzikinta gaba.

Duniya
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

June 9, 2026
Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima
Manyan Labarai

Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima

June 9, 2026
Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

June 8, 2026
Next Post
Rayuwar Annabi Muhammadu (SAW) Da Abin Da Ya Ta’allaka Da Aurensa (2)

Rayuwar Annabi Muhammadu (SAW) Da Abin Da Ya Ta’allaka Da Aurensa (2)

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

June 9, 2026
Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima

Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima

June 9, 2026
Sojoji

Ilimi Ne Babban Makamin Daƙile Ta’addanci — Ministan Tsaro

June 8, 2026
Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

June 8, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Gwamnatin Borno Ta Musanta Biyan Kuɗin Fansa Domin Kuɓutar da Mutane 360

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

June 8, 2026
Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

June 8, 2026
Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

June 8, 2026
Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

June 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.