• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Kudin Shiga Na Naira Tirililan 34.8 A 2025

by Yusuf Shuaibu
9 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Kudin Shiga Na Naira Tirililan 34.8 A 2025
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya na hasashen samun kudin shiga na naira tiriliyan 34.8 a kudirin kasafin kudin 2025. Kudirin ya kuma tsara dabarun sake fasalin bashi da nufin ‘yantar da kudade don ci gaban ababen more rayuwa.

Wannan tsarin yana daya daga cikin muhimman abubuwan da aka tsara na 2025-2027, matsakaaicin dubarun harkokin kudade, wanda majalisar zartarwa ta tarayya ta amince da shi a ranar Alhamis.

  • Gwamnati Ta ÆŠage Haramcin Tura Masu Yi Wa Ƙasa Hidima Bankuna Da Sauran Masana’antu 
  • Zargin Tarayya Da Matar Aure: Miji Ya Ki Amincewa Da Hukuncin Kotun Da Ta Wanke Kwamishinan Jigawa

Za a mika kudirin kasafin kudin 2025 na naira tiriliyan 47.9 ga majalisar dokoki ta kasa domin tantancewa.

A cewar takardar da ofishin kasafin kudi na tarayya ya fitar, ana sa ran biyan basussuka, saboda yawan basussukan da ake bin kasar da kuma yadda babban bankin Nijeriya (CBN) ya kara kudin ruwa zuwa kashi 27.25.

Kudirin dokar ya zayyana yadda za a samu manyan kudaden shiga da manufofin kashewa a cikin 2025.

Labarai Masu Nasaba

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

A karkashin kudaden shiga, gwamnatin tarayya na shirin samun naira tiriliyan 34.8 da naira tiriliyan 19.6 da naira tiriliyan 5.7 daga harajin man fetur da bangarori wadanda ba na man fetur ba, naira tiriliyan 2.87 daga kamfanonin mallakar gwamnati, naira tiriliyan 3.6 daga hanyoyin samun kudaden shiga masu zaman kansu da kuma naira tiriliyan 4.8 daga wasu hanyoyin.

Kudirin kashe kudi na gwamnati na shekara mai zuwa shi ne naira tiriliyan 47.9, wanda ya kunshi naira tiriliyan 14.2 na biyan bashi, naira tiriliyan 16.4 za a kashe wajen gudanar da manyan ayyuka, naira tiriliyan 15.38 na hidimar basussuka da kuma naira tiriliyan 2 na sauran abubuwan da za a yi.

Gwamnati ta amince da kalubalen tattara kudaden shiga, karancin mai da iskar gas, da hauhawar farashin tallafin man fetur a matsayin masu bayar da gudummawa ga gibin kasafin kudin tarayya.

Sai dai ana sa ran sauye-sauyen da aka yi a baya-bayan nan da suka hada da cire tallafin man fetur, da rage harajin da ake samu, da karuwar yawan danyen mai da ake hakowa za su rage matsin tattalin arziki.

Domin cike gibin kasafin kudin, gwamnati za ta ciyo bashi mai sassauci da kuma aiwatar da matakan tattara kudaden shiga.

Gwamnati na shirin kara zage damtse wajen inganta harkokin kudi ta hanyar karfafa tsarin kasafin kudi da kuma duba yadda ma’aikatu da hukumomi gwamnati suke kashe kudade.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: gwamnatiTarayya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Halartar Shugaba Xi Taron APEC Da G20, Da Ziyarar Aiki A Peru Da Brazil Sun Kasance Wata Hanyar Sada Zumunta Da Hadin Gwiwa

Next Post

Firaministan Kasar Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar Sin

Related

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

5 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

6 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da ÆŠansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

7 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da ÆŠansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

8 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

9 hours ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da ÆŠansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

10 hours ago
Next Post
Firaministan Kasar Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar Sin

Firaministan Kasar Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.