ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Kudin Shiga Na Naira Tirililan 34.8 A 2025

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Tarayya

Gwamnatin tarayya na hasashen samun kudin shiga na naira tiriliyan 34.8 a kudirin kasafin kudin 2025. Kudirin ya kuma tsara dabarun sake fasalin bashi da nufin ‘yantar da kudade don ci gaban ababen more rayuwa.

Wannan tsarin yana daya daga cikin muhimman abubuwan da aka tsara na 2025-2027, matsakaaicin dubarun harkokin kudade, wanda majalisar zartarwa ta tarayya ta amince da shi a ranar Alhamis.

  • Gwamnati Ta Ɗage Haramcin Tura Masu Yi Wa Ƙasa Hidima Bankuna Da Sauran Masana’antu 
  • Zargin Tarayya Da Matar Aure: Miji Ya Ki Amincewa Da Hukuncin Kotun Da Ta Wanke Kwamishinan Jigawa

Za a mika kudirin kasafin kudin 2025 na naira tiriliyan 47.9 ga majalisar dokoki ta kasa domin tantancewa.

ADVERTISEMENT

A cewar takardar da ofishin kasafin kudi na tarayya ya fitar, ana sa ran biyan basussuka, saboda yawan basussukan da ake bin kasar da kuma yadda babban bankin Nijeriya (CBN) ya kara kudin ruwa zuwa kashi 27.25.

Kudirin dokar ya zayyana yadda za a samu manyan kudaden shiga da manufofin kashewa a cikin 2025.

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

A karkashin kudaden shiga, gwamnatin tarayya na shirin samun naira tiriliyan 34.8 da naira tiriliyan 19.6 da naira tiriliyan 5.7 daga harajin man fetur da bangarori wadanda ba na man fetur ba, naira tiriliyan 2.87 daga kamfanonin mallakar gwamnati, naira tiriliyan 3.6 daga hanyoyin samun kudaden shiga masu zaman kansu da kuma naira tiriliyan 4.8 daga wasu hanyoyin.

Kudirin kashe kudi na gwamnati na shekara mai zuwa shi ne naira tiriliyan 47.9, wanda ya kunshi naira tiriliyan 14.2 na biyan bashi, naira tiriliyan 16.4 za a kashe wajen gudanar da manyan ayyuka, naira tiriliyan 15.38 na hidimar basussuka da kuma naira tiriliyan 2 na sauran abubuwan da za a yi.

Gwamnati ta amince da kalubalen tattara kudaden shiga, karancin mai da iskar gas, da hauhawar farashin tallafin man fetur a matsayin masu bayar da gudummawa ga gibin kasafin kudin tarayya.

Sai dai ana sa ran sauye-sauyen da aka yi a baya-bayan nan da suka hada da cire tallafin man fetur, da rage harajin da ake samu, da karuwar yawan danyen mai da ake hakowa za su rage matsin tattalin arziki.

Domin cike gibin kasafin kudin, gwamnati za ta ciyo bashi mai sassauci da kuma aiwatar da matakan tattara kudaden shiga.

Gwamnati na shirin kara zage damtse wajen inganta harkokin kudi ta hanyar karfafa tsarin kasafin kudi da kuma duba yadda ma’aikatu da hukumomi gwamnati suke kashe kudade.

Tarayya
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Next Post
Firaministan Kasar Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar Sin

Firaministan Kasar Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.