ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Kudin Shiga Na Naira Tirililan 34.8 A 2025

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Tarayya

Gwamnatin tarayya na hasashen samun kudin shiga na naira tiriliyan 34.8 a kudirin kasafin kudin 2025. Kudirin ya kuma tsara dabarun sake fasalin bashi da nufin ‘yantar da kudade don ci gaban ababen more rayuwa.

Wannan tsarin yana daya daga cikin muhimman abubuwan da aka tsara na 2025-2027, matsakaaicin dubarun harkokin kudade, wanda majalisar zartarwa ta tarayya ta amince da shi a ranar Alhamis.

  • Gwamnati Ta Ɗage Haramcin Tura Masu Yi Wa Ƙasa Hidima Bankuna Da Sauran Masana’antu 
  • Zargin Tarayya Da Matar Aure: Miji Ya Ki Amincewa Da Hukuncin Kotun Da Ta Wanke Kwamishinan Jigawa

Za a mika kudirin kasafin kudin 2025 na naira tiriliyan 47.9 ga majalisar dokoki ta kasa domin tantancewa.

ADVERTISEMENT

A cewar takardar da ofishin kasafin kudi na tarayya ya fitar, ana sa ran biyan basussuka, saboda yawan basussukan da ake bin kasar da kuma yadda babban bankin Nijeriya (CBN) ya kara kudin ruwa zuwa kashi 27.25.

Kudirin dokar ya zayyana yadda za a samu manyan kudaden shiga da manufofin kashewa a cikin 2025.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

A karkashin kudaden shiga, gwamnatin tarayya na shirin samun naira tiriliyan 34.8 da naira tiriliyan 19.6 da naira tiriliyan 5.7 daga harajin man fetur da bangarori wadanda ba na man fetur ba, naira tiriliyan 2.87 daga kamfanonin mallakar gwamnati, naira tiriliyan 3.6 daga hanyoyin samun kudaden shiga masu zaman kansu da kuma naira tiriliyan 4.8 daga wasu hanyoyin.

Kudirin kashe kudi na gwamnati na shekara mai zuwa shi ne naira tiriliyan 47.9, wanda ya kunshi naira tiriliyan 14.2 na biyan bashi, naira tiriliyan 16.4 za a kashe wajen gudanar da manyan ayyuka, naira tiriliyan 15.38 na hidimar basussuka da kuma naira tiriliyan 2 na sauran abubuwan da za a yi.

Gwamnati ta amince da kalubalen tattara kudaden shiga, karancin mai da iskar gas, da hauhawar farashin tallafin man fetur a matsayin masu bayar da gudummawa ga gibin kasafin kudin tarayya.

Sai dai ana sa ran sauye-sauyen da aka yi a baya-bayan nan da suka hada da cire tallafin man fetur, da rage harajin da ake samu, da karuwar yawan danyen mai da ake hakowa za su rage matsin tattalin arziki.

Domin cike gibin kasafin kudin, gwamnati za ta ciyo bashi mai sassauci da kuma aiwatar da matakan tattara kudaden shiga.

Gwamnati na shirin kara zage damtse wajen inganta harkokin kudi ta hanyar karfafa tsarin kasafin kudi da kuma duba yadda ma’aikatu da hukumomi gwamnati suke kashe kudade.

Tarayya
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Firaministan Kasar Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar Sin

Firaministan Kasar Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.