• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ban Ce Ina Goyon Bayan Dokar Haraji Dari Bisa Dari Ba – Kofa

by Sadiq
11 months ago
Haraji

Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Kiru da Bebeji, Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ya bayyana cewa bai taba goyon bayan dokar gyaran haraji dari bisa dari ba, inda ya bai wa jama’a hakuri kan lamarin.

Ya ce: “Abin da na fada shi ne, akwai abubuwa da dama a cikin dokar da za su amfani Arewa da Nijeriya baki daya.

  • Majalisar Wakilai Ta Dakatar Da CBN Daga Sallamar Ma’aikata 1000
  • Adadin Zirga Zirga Ta Jiragen Kasa A Sin Ya Haura Biliyan 4 A Watanni 11 Na Farkon Bana

“Mu, ‘yan Majalisar Arewa, ya kamata mu yi amfani da rinjayenmu wajen tabbatar da cewa duk abin da zai amfani yankinmu mun goyi bayansa.

“Idan kuma akwai wani bangare da zai cutar da mu, sai mu gyara ko mu cire shi.”

Wannan bayanin na cikin wata takarda da ya fitar a Kano a ranar Laraba.

LABARAI MASU NASABA

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

Ya kara da cewa: “Ya kamata mu yi amfani da wannan dama wajen bijiro da wasu dokoki da za su amfani Arewa, a kuma tabbatar da cewa an yi wa sauran jihohi adalci.

“Amma wasu na ganin ya kamata a yi watsi da dokar gaba daya.”

Kofa ya jaddada cewa: “A matsayina na wakili, ban taba goyon bayan wata doka da za ta cutar da al’ummata ba, kuma ba zan taba yi ba,” in ji shi.

“Duk wanda ya ji haushin matsayata, ina ba shi hakuri, musamman abokan aikina ‘yan majalisa, Sanatoci, gwamnoni, shugabanni, sarakuna, malamai, ‘yan kasuwa, ‘yan siyasa, ‘yan boko, ‘yan jarida, mata da matasa. Allah Ya kara mana fahimta.”

Ya kuma gode wa jagoran NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, bisa shawarwari da goyon baya da yake ba shi, tare da gode wa Alkali Salihu Abubakar daga Jamila Zariya bisa jajircewarsu wajen faɗakarwa.

“Zan ci gaba da kokarin ganin ba a cutar da Arewa ba, kuma an yi wa kowa adalci a Nijeriya,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya
Manyan Labarai

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?
Manyan Labarai

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Next Post
Akwai Bukatar Mu Bai Wa Mbappe Lokaci Domin Dawowa Kan Ganiyarsa – Ancelotti 

Akwai Bukatar Mu Bai Wa Mbappe Lokaci Domin Dawowa Kan Ganiyarsa - Ancelotti 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025
Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

November 4, 2025
China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.