A yau Litinin ne ofishin hukumar siyasa ta kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, ya kira taron nazari da duba ayyukan raya tattalin arziki na shekarar 2025, da tsara yanayin ayyukan jam’iyya da ayyukan yaki da cin hanci.
Shugaban kasar Sin kuma babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, Xi Jinping ne, ya jagoranci zaman. (Saminu Alhassan)