ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Rantsar Da Sabon Kwamishina Tare Da Yin Garambawul Ga Muƙarrabansa

by Sulaiman
2 years ago
Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal ya yi garambawul a gwamnatinsa, sannan ya rantsar da wani sabon Kwamishina.

 

A Litinin ɗin nan ne Gwamna Dauda Lawal ya jagoranci zaman majalisar zartarwar jihar, inda a lokacin zaman ya rantsar da wani sabon Kwamishina.

ADVERTISEMENT
  • Kamfanin Turkiyya Ya Fara Aikin inganta Noman Zamani A Zamfara 
  • Kebbi Da Brazil Zasu Yi Haɗin Gwuiwa Kan Sarrafa Nama Ta Hanyar Zamani

A cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana cewa a wannan zaman Majalisar, gwamnan ya canja wa wasu Kwamishinoni wuraren aiki.

Sanarwar ta ce, an naɗa sabon Kwamishinan, Kasimu Sani Kaura ne don ya maye girbin Mannir Muazu Haidara, wanda ya ajiye aiki, kuma aka zaɓe shi a matsayin Shugaban Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda.

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Gwamna Lawal ya bayyana wa Majalisar cewa dacewa ce ta sa aka zaɓo Kasimu Sani Kaura don ya wakilci al’ummar Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda a Majalisar, wanda kuma ya kasance mutum ne jajirtacce game da ci gaban al’ummarsa, da ma jihar baki ɗaya.

Gwamnan ya ce, “Wannan naɗi, wata alamar tabbaci ce ta gwamnatin nan na zaƙulo jajirtattun mutanen da za su bayar da gagarumar gudumawa wajen inganta rayuwar al’umma da ci gaban jihar Zamfara.

“Ina mai yin kira ga sabon Kwamishinan kan ya bayar da rayuwarsa wajen yi wa al’ummar sa hidima. A matsayin sa na mamba a harkar ceto jihar Zamfara, ba ni da shakkun irin gagarumar gudumawar da zai bayar don amfanin jama’a.

“Mai girma Kwamishina, ina taya ka murnar wannan kira da aka yi maka don ka yi wa al’umma hidama. Ina maka, tare da dukkan mu fatan tsarewar Allah. Ina mai kira gare ka da ka kasance kana aiki kafaɗa da kafaɗa tare da sauran Kwamishinoni, da kuma ma’aikatan ma’aikatarka.

Gwamnan ya ce, ya lura da yadda dukkan muƙarrabansa ke gudanar da ayyukansu, wanda hakan ne ta sa ya yi wasu ‘yan canje-canje. “Don ganin mun samu nasarar sauke nauyin da ke kanmu, ina ganin akwai buƙatuwar yin wasu ‘yan canje-canje a gwamnatina.”

“Wannan sabon Kwamishina, Kasimu Sani Kaura, zai kula da ma’aikatar muhalli da albarkatun ƙasa, inda ya maye gurbin Hon. Mahmud Mohammed Abdullahi, Wanda aka mayar da shi mai kula da ma’aikatar yaɗa labarai da al’adu.

“Hon. Nasiru Ibrahim Zurmi kuma ya koma Kwamishina a ma’aikatar kula da birane, inda ya maye gurbin Hon. Kabiru Moyi, wanda ya koma. Ma’aikatar sanya ido da aiwatar da ayyuka.

“Bugu da ƙari, an canja Dr. Nafisa Muhammad zuwa ma’aikatar lafiya, inda ta maye gurbin Dr. Aisha M. Za Anka, wacce ta koma Kwamishina a ma’aikatar kula da mata da inganta jin daɗin jama’a.

“Za a kammala duk wasu shirye-shiryen miƙa shugabancin a tsakanin kwanaki bakwai. Ina so in ƙara tunatar da ku cewa zan ci gaba da sanya ido da yadda kuke gudanarwa, tare da auna ayyukanku, domin muna fuskantar rabin wa’adinmu a ofis. Mu yi amfani da wannan dama wajen jajircewa da sadaukarwa wajen yi wa jihar mu ta Zamfara hidima.”

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Next Post
Jagororin Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Sun Gudanar Da Taron Nazarin Tattalin Arziki Da Ayyukan Jam’iyya Da Yaki Da Cin Hanci Na 2025

Jagororin Jam'iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Sun Gudanar Da Taron Nazarin Tattalin Arziki Da Ayyukan Jam'iyya Da Yaki Da Cin Hanci Na 2025

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.