ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Rantsar Da Sabon Kwamishina Tare Da Yin Garambawul Ga Muƙarrabansa

by Sulaiman
1 year ago
Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal ya yi garambawul a gwamnatinsa, sannan ya rantsar da wani sabon Kwamishina.

 

A Litinin ɗin nan ne Gwamna Dauda Lawal ya jagoranci zaman majalisar zartarwar jihar, inda a lokacin zaman ya rantsar da wani sabon Kwamishina.

ADVERTISEMENT
  • Kamfanin Turkiyya Ya Fara Aikin inganta Noman Zamani A Zamfara 
  • Kebbi Da Brazil Zasu Yi Haɗin Gwuiwa Kan Sarrafa Nama Ta Hanyar Zamani

A cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana cewa a wannan zaman Majalisar, gwamnan ya canja wa wasu Kwamishinoni wuraren aiki.

Sanarwar ta ce, an naɗa sabon Kwamishinan, Kasimu Sani Kaura ne don ya maye girbin Mannir Muazu Haidara, wanda ya ajiye aiki, kuma aka zaɓe shi a matsayin Shugaban Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Gwamna Lawal ya bayyana wa Majalisar cewa dacewa ce ta sa aka zaɓo Kasimu Sani Kaura don ya wakilci al’ummar Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda a Majalisar, wanda kuma ya kasance mutum ne jajirtacce game da ci gaban al’ummarsa, da ma jihar baki ɗaya.

Gwamnan ya ce, “Wannan naɗi, wata alamar tabbaci ce ta gwamnatin nan na zaƙulo jajirtattun mutanen da za su bayar da gagarumar gudumawa wajen inganta rayuwar al’umma da ci gaban jihar Zamfara.

“Ina mai yin kira ga sabon Kwamishinan kan ya bayar da rayuwarsa wajen yi wa al’ummar sa hidima. A matsayin sa na mamba a harkar ceto jihar Zamfara, ba ni da shakkun irin gagarumar gudumawar da zai bayar don amfanin jama’a.

“Mai girma Kwamishina, ina taya ka murnar wannan kira da aka yi maka don ka yi wa al’umma hidama. Ina maka, tare da dukkan mu fatan tsarewar Allah. Ina mai kira gare ka da ka kasance kana aiki kafaɗa da kafaɗa tare da sauran Kwamishinoni, da kuma ma’aikatan ma’aikatarka.

Gwamnan ya ce, ya lura da yadda dukkan muƙarrabansa ke gudanar da ayyukansu, wanda hakan ne ta sa ya yi wasu ‘yan canje-canje. “Don ganin mun samu nasarar sauke nauyin da ke kanmu, ina ganin akwai buƙatuwar yin wasu ‘yan canje-canje a gwamnatina.”

“Wannan sabon Kwamishina, Kasimu Sani Kaura, zai kula da ma’aikatar muhalli da albarkatun ƙasa, inda ya maye gurbin Hon. Mahmud Mohammed Abdullahi, Wanda aka mayar da shi mai kula da ma’aikatar yaɗa labarai da al’adu.

“Hon. Nasiru Ibrahim Zurmi kuma ya koma Kwamishina a ma’aikatar kula da birane, inda ya maye gurbin Hon. Kabiru Moyi, wanda ya koma. Ma’aikatar sanya ido da aiwatar da ayyuka.

“Bugu da ƙari, an canja Dr. Nafisa Muhammad zuwa ma’aikatar lafiya, inda ta maye gurbin Dr. Aisha M. Za Anka, wacce ta koma Kwamishina a ma’aikatar kula da mata da inganta jin daɗin jama’a.

“Za a kammala duk wasu shirye-shiryen miƙa shugabancin a tsakanin kwanaki bakwai. Ina so in ƙara tunatar da ku cewa zan ci gaba da sanya ido da yadda kuke gudanarwa, tare da auna ayyukanku, domin muna fuskantar rabin wa’adinmu a ofis. Mu yi amfani da wannan dama wajen jajircewa da sadaukarwa wajen yi wa jihar mu ta Zamfara hidima.”

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • Sulaiman
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Jagororin Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Sun Gudanar Da Taron Nazarin Tattalin Arziki Da Ayyukan Jam’iyya Da Yaki Da Cin Hanci Na 2025

Jagororin Jam'iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Sun Gudanar Da Taron Nazarin Tattalin Arziki Da Ayyukan Jam'iyya Da Yaki Da Cin Hanci Na 2025

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.