• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rai Da Lafiyar Mazajenmu Ya Fi Mana Jarumtarsu

by Mairo Muhammad Mudi
6 months ago
in Labarai
0
Rai Da Lafiyar Mazajenmu Ya Fi Mana Jarumtarsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani al’amari mai ban tsoro da ke faruwa a halin yanzu shi ne, yadda babu zato babu tsammani, ba kuma tare da wata alama ba; kwatam, sai ka ga maza sun fadi ringis; sun kasa mikewa.

A cikin shekarun baya-bayan nan, mun ga yadda wasu maza lafiyayyu; masu kuzari a jiki ke faduwa yayin gudanar da ayyukan motsa jiki. Wannan al’amari mai tayar da hankali, na ci gaba da yawaita a tsakanin al’umma tare da kawo mana bakin ciki a cikin rayuwarmu.

  • Kidayar Jama’a Da Harkar Lafiya
  • Sin Ta Yi Maraba Da Amincewar Da UNGA Ya Yi Da Kudurin Wanzar Da Zaman Lafiya Da Kasar Ta Gabatar

Haka zalika, ba wai maza kadai ne irin wannan mutuwa ta fuju’an ke faruwa da su ba; har ma da matan, illa kawai dai na mazan ya fi rinjayar na mazan a zahiri.

A ‘yan shekarun nan, wani abin bakin ciki da takaici da har yanzu yana nan a raina shi ne, wani dan’uwan maigidana ne; wanda a zahiri mutum ne lafiyayye kuma dogo, dan wasan kwallon kwando, ya kasance kuma tauraro a kwallon kwandon; wanda yake wakiltar jiharmu da kuma kasa baki-daya.

Har ila yau, duk wanda ya kalle shi; zai ga lafiya ce ke tafiya karara tare da sha’awarsa; sakamakon ganin sa da ake yi yana motsa jiki a kowace yamma ta duniya, amma sai rashin sa’a ta taru da shi a ranar wata Alhamis, inda babu zato; babu tsammani ya yanke jiki ya fadi a filin wasa yana dauke da Azumi, tun daga nan bai sake motsawa ba; haka muka rasa shi.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

Haka nan, Dakta Mahmoud Muhammad; tsohon babban likitan asibitin IBB, sannan kuma tsohon babban sakatare a Jihar Neja, wanda shi ma tasa mutuwar ta yi matukar girgiza al’umma, wanda a cikin wani bidiyo mai tayar da hankali ya nuna shi cikin kuzari, yana buga kwallo a wani filin kwallo; kamar wani kwararren dan wasa, amma kafin kiftawar ido; ya fadi kasa, kamar wanda ya gaji yake son hutawa, sai kuma wannan ce kwanciyar tasa ta har abada.

Kazalika, shi ma wani sanannen matashi dan Kannywood; mai cike da kuzari, El-Muaz Muhammad; ya rasa rayuwarsa yayin da yake yin wannan wasa na kwallo, inda nan take ya fadi babu zato; babu tsammani, daga nan kuma sai ya ce ga garinku.

Irin wadannan abubuwan bakin ciki, na ci gaba da yawaita a takanin al’ummarmu. Wannan yasa nake tambayar abin da ke haddasa ire-iren wannan mutuwa ta fuji’an a tsakanin mazajenmu.

A matsayina na Musulma, na yarda da fadin Allah SWT cewa; “Kullu nafsin za’ikatul maut”, ma’ana; kowane mai rai zai dandani mutuwa, kuma babu wanda zai bar duniya kafin lokacinsa ya yi, amma duk da haka kuma, imaninmu ba zai taba cire mana alhakin kula da lafiyarmu ba.

Wadannan asarar rayukan da muke yi na mazajenmu, dole ne na yi kira da mu farka, musamman ma ga maza; wadanda galibi ke yin sakaci wajen kula da lafiyarsu, suna barin matansu na ci gaba da kasancewa a matsayin zawarawa; ‘ya’yansu kuma na zama marayu.

A al’ada, mun yarda da cewa; mutuwa ba ta da makawa, duk wanda lokacinsa ya yi; wajibi ne ya tafi. Sai dai abin mamaki kuma shi ne, yayin da muke kokarin jinkirta ko kauce mata, wasu daga cikin ayyukanmu na rashin sani; kan sanya mu matsa kusa da ita da gangan. Misali, muna kula da motocinmu da kyau kafin mu fara tafiya da su, haka nan ba za mu taba kwanciya a kan hanya ba, saboda zai kasance tamkar kisan kai ne.

Amma duk da haka, maza da yawa na yin sakaci da lafiyarsu, ba tare da suna kula da ita yadda ya kamata ba, suna kai kansu ga hadarin da ya kamata su rika gujewa.

A lokacin da nake aiki a ofishin jin kai na Asibitin Suleja, na lura da bambanci mai ban mamaki. Ofishinmu na kusa da dakin kula da masu ciwon hawan jini, a nan ne na fara lura cewa; galibin marasa lafiya mata ne. Wannan yasa na yi tunanin cewa, mata sun fi maza samun cutar hawan jinni; saboda damuwar da ke tattare da aure da rainon yara ga uwa.

Amma daga bisani, sai na gano cewa; yayin da mata ke zuwa neman magani idan ba su da lafiya ko suna dauke da juna biyu, maza kan yi shiru ne da bakinsu, ciwo na damunsu amma saboda kokarin nuna jarumta; sai su yi shiru har sai ya illata su.

Don haka, ya kamata maza su sani cewa; mu danginku muna bukatar ku cikin koshin lafiya, bai kamata ku rika sadaukar da rayuwarku; kuna matsa wa kanku wajen yin aiki tukuru ba, alhali jikinku yana son hutu.

Ku fara da yin gwaje-gwajen lafiyarku akai-akai a asibiti ko kuma a gida. Yanzu Bature ya kawo mana sauki, domin kuwa za ka iya sayen na’ura mai sarrafa kanta a cikin sauki wajen gwajin hawan jini da ciwon suga, sannan wannan na’ura za ta iya taimaka muku wajen samun bayanai ko shawarar ganin likita nan take; ko kuma batun daukar huta kafin ci gaba da motsa jikin da kuke yi na yau da gobe.

A nan, ba wai ina cewa wannan zai maye gurbin shawarar likita ba ne, amma zai iya zama tamkar wata fadakarwa ce mai matukar amfani; don neman taimakon gaggawa.

A takaice dai, ku kasance kuna cikin koshin lafiya; ku rika samun lokacin hutawa yadda ya kamata, sannan kuma ku tabbata kun kasance masu bayyana wa wadanda kuka yarda da su matsalolin da suke addabar ku.

Akwai alamomin da jikinku zai fada muku a daidai lokacin da kuke bukatar hutu; ku yi na’am da wannan sako, domin rayuwarku kyauta ce; lafiyarku kuma ba kawai taku ba ce, har ma da wadanda ke kaunarku.

Mazaje a manta da jarumtaka a bai wa jiki hakkinsa. Ku tabbata kuna hutawa a duk yayin da kuka gaji, idan jiki na yi muku ciwo; a yi maza a ga likita. Ba ma bukatar jarumtakarka, domin mun fi mukatarku da rai da kuma koshin lafiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Lafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Muhimmiyar Makalar Xi Mai Taken “Zurfafa Aiwatar Da Juyin Juya Halin Jam’iyyar Kwaminis Ta Sin”

Next Post

ASUU Reshen Jami’ar Sa’adu Zungur Ta Dakatar Da Yajin Aiki

Related

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

1 hour ago
bakin wake
Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

3 hours ago
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar
Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

6 hours ago
Gwamnan kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

7 hours ago
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina
Labarai

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

7 hours ago
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya
Labarai

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

8 hours ago
Next Post
ASUU Reshen Jami’ar Sa’adu Zungur Ta Dakatar Da Yajin Aiki

ASUU Reshen Jami'ar Sa'adu Zungur Ta Dakatar Da Yajin Aiki

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

June 1, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

June 1, 2025
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

June 1, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

June 1, 2025
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

June 1, 2025
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.