• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rai Da Lafiyar Mazajenmu Ya Fi Mana Jarumtarsu

by Mairo Muhammad Mudi
10 months ago
in Labarai
0
Rai Da Lafiyar Mazajenmu Ya Fi Mana Jarumtarsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani al’amari mai ban tsoro da ke faruwa a halin yanzu shi ne, yadda babu zato babu tsammani, ba kuma tare da wata alama ba; kwatam, sai ka ga maza sun fadi ringis; sun kasa mikewa.

A cikin shekarun baya-bayan nan, mun ga yadda wasu maza lafiyayyu; masu kuzari a jiki ke faduwa yayin gudanar da ayyukan motsa jiki. Wannan al’amari mai tayar da hankali, na ci gaba da yawaita a tsakanin al’umma tare da kawo mana bakin ciki a cikin rayuwarmu.

  • Kidayar Jama’a Da Harkar Lafiya
  • Sin Ta Yi Maraba Da Amincewar Da UNGA Ya Yi Da Kudurin Wanzar Da Zaman Lafiya Da Kasar Ta Gabatar

Haka zalika, ba wai maza kadai ne irin wannan mutuwa ta fuju’an ke faruwa da su ba; har ma da matan, illa kawai dai na mazan ya fi rinjayar na mazan a zahiri.

A ‘yan shekarun nan, wani abin bakin ciki da takaici da har yanzu yana nan a raina shi ne, wani dan’uwan maigidana ne; wanda a zahiri mutum ne lafiyayye kuma dogo, dan wasan kwallon kwando, ya kasance kuma tauraro a kwallon kwandon; wanda yake wakiltar jiharmu da kuma kasa baki-daya.

Har ila yau, duk wanda ya kalle shi; zai ga lafiya ce ke tafiya karara tare da sha’awarsa; sakamakon ganin sa da ake yi yana motsa jiki a kowace yamma ta duniya, amma sai rashin sa’a ta taru da shi a ranar wata Alhamis, inda babu zato; babu tsammani ya yanke jiki ya fadi a filin wasa yana dauke da Azumi, tun daga nan bai sake motsawa ba; haka muka rasa shi.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Haka nan, Dakta Mahmoud Muhammad; tsohon babban likitan asibitin IBB, sannan kuma tsohon babban sakatare a Jihar Neja, wanda shi ma tasa mutuwar ta yi matukar girgiza al’umma, wanda a cikin wani bidiyo mai tayar da hankali ya nuna shi cikin kuzari, yana buga kwallo a wani filin kwallo; kamar wani kwararren dan wasa, amma kafin kiftawar ido; ya fadi kasa, kamar wanda ya gaji yake son hutawa, sai kuma wannan ce kwanciyar tasa ta har abada.

Kazalika, shi ma wani sanannen matashi dan Kannywood; mai cike da kuzari, El-Muaz Muhammad; ya rasa rayuwarsa yayin da yake yin wannan wasa na kwallo, inda nan take ya fadi babu zato; babu tsammani, daga nan kuma sai ya ce ga garinku.

Irin wadannan abubuwan bakin ciki, na ci gaba da yawaita a takanin al’ummarmu. Wannan yasa nake tambayar abin da ke haddasa ire-iren wannan mutuwa ta fuji’an a tsakanin mazajenmu.

A matsayina na Musulma, na yarda da fadin Allah SWT cewa; “Kullu nafsin za’ikatul maut”, ma’ana; kowane mai rai zai dandani mutuwa, kuma babu wanda zai bar duniya kafin lokacinsa ya yi, amma duk da haka kuma, imaninmu ba zai taba cire mana alhakin kula da lafiyarmu ba.

Wadannan asarar rayukan da muke yi na mazajenmu, dole ne na yi kira da mu farka, musamman ma ga maza; wadanda galibi ke yin sakaci wajen kula da lafiyarsu, suna barin matansu na ci gaba da kasancewa a matsayin zawarawa; ‘ya’yansu kuma na zama marayu.

A al’ada, mun yarda da cewa; mutuwa ba ta da makawa, duk wanda lokacinsa ya yi; wajibi ne ya tafi. Sai dai abin mamaki kuma shi ne, yayin da muke kokarin jinkirta ko kauce mata, wasu daga cikin ayyukanmu na rashin sani; kan sanya mu matsa kusa da ita da gangan. Misali, muna kula da motocinmu da kyau kafin mu fara tafiya da su, haka nan ba za mu taba kwanciya a kan hanya ba, saboda zai kasance tamkar kisan kai ne.

Amma duk da haka, maza da yawa na yin sakaci da lafiyarsu, ba tare da suna kula da ita yadda ya kamata ba, suna kai kansu ga hadarin da ya kamata su rika gujewa.

A lokacin da nake aiki a ofishin jin kai na Asibitin Suleja, na lura da bambanci mai ban mamaki. Ofishinmu na kusa da dakin kula da masu ciwon hawan jini, a nan ne na fara lura cewa; galibin marasa lafiya mata ne. Wannan yasa na yi tunanin cewa, mata sun fi maza samun cutar hawan jinni; saboda damuwar da ke tattare da aure da rainon yara ga uwa.

Amma daga bisani, sai na gano cewa; yayin da mata ke zuwa neman magani idan ba su da lafiya ko suna dauke da juna biyu, maza kan yi shiru ne da bakinsu, ciwo na damunsu amma saboda kokarin nuna jarumta; sai su yi shiru har sai ya illata su.

Don haka, ya kamata maza su sani cewa; mu danginku muna bukatar ku cikin koshin lafiya, bai kamata ku rika sadaukar da rayuwarku; kuna matsa wa kanku wajen yin aiki tukuru ba, alhali jikinku yana son hutu.

Ku fara da yin gwaje-gwajen lafiyarku akai-akai a asibiti ko kuma a gida. Yanzu Bature ya kawo mana sauki, domin kuwa za ka iya sayen na’ura mai sarrafa kanta a cikin sauki wajen gwajin hawan jini da ciwon suga, sannan wannan na’ura za ta iya taimaka muku wajen samun bayanai ko shawarar ganin likita nan take; ko kuma batun daukar huta kafin ci gaba da motsa jikin da kuke yi na yau da gobe.

A nan, ba wai ina cewa wannan zai maye gurbin shawarar likita ba ne, amma zai iya zama tamkar wata fadakarwa ce mai matukar amfani; don neman taimakon gaggawa.

A takaice dai, ku kasance kuna cikin koshin lafiya; ku rika samun lokacin hutawa yadda ya kamata, sannan kuma ku tabbata kun kasance masu bayyana wa wadanda kuka yarda da su matsalolin da suke addabar ku.

Akwai alamomin da jikinku zai fada muku a daidai lokacin da kuke bukatar hutu; ku yi na’am da wannan sako, domin rayuwarku kyauta ce; lafiyarku kuma ba kawai taku ba ce, har ma da wadanda ke kaunarku.

Mazaje a manta da jarumtaka a bai wa jiki hakkinsa. Ku tabbata kuna hutawa a duk yayin da kuka gaji, idan jiki na yi muku ciwo; a yi maza a ga likita. Ba ma bukatar jarumtakarka, domin mun fi mukatarku da rai da kuma koshin lafiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Lafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Muhimmiyar Makalar Xi Mai Taken “Zurfafa Aiwatar Da Juyin Juya Halin Jam’iyyar Kwaminis Ta Sin”

Next Post

ASUU Reshen Jami’ar Sa’adu Zungur Ta Dakatar Da Yajin Aiki

Related

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara
Tsaro

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

1 hour ago
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa
Labarai

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

2 hours ago
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya
Labarai

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

3 hours ago
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC
Labarai

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

4 hours ago
Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya
Labarai

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

7 hours ago
Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa
Labarai

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

8 hours ago
Next Post
ASUU Reshen Jami’ar Sa’adu Zungur Ta Dakatar Da Yajin Aiki

ASUU Reshen Jami'ar Sa'adu Zungur Ta Dakatar Da Yajin Aiki

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

October 5, 2025
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

October 5, 2025
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.