• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an Tsaron Nijeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 8,034 A 2024 – ONSA

by Khalid Idris Doya, Sulaiman and Bello Hamza
11 months ago
ONSA

Ofishin Mashawarcin Shugaban Kasa kan harkokin tsaro (ONSA) ta ce, bisa azama da himmar hadakar jami’an tsaron soji, ‘yansanda da sauran hukumomin tsaro hakan ya kai ga nasarar kawo karshen ‘yan ta’adda 8,034 a shekarar 2024.

Har ila yau, ONSA ta ce, ayyukan hukumomin ya kuma kai ga cafke mutum 11,623 da ake zargin ‘yan ta’adda ne kari da ceto mutane 7,967 da aka yi garkuwa da su a shekarar 2024.

  • Mun Karbi Rancen Dala Biliyan 1 Don Tallafa Wa Matatar Man Dangote —NNPC
  • Dakarun MNJTF Sun Daƙile Harin Da Aka Kai Sansanin Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 10 A Kamaru

Daraktan kwamitin lamuran shari’a da dabarun sadarwa na ofishin Mashawarcin Shugaban Kasan, Zakari Mijinyawa, shi ne ya shaida hakan a lokacin da ke ganawa da ‘yan jarida a ranar Litinin a Abuja.

Mijinyawa ya kara kuma da cewa yunkurin jami’an tsaron ya kuma haifar da sakamakon mai kyau na kwato makamai 10,200 da alburusai 224,709 daga hannun ‘yan ta’addan dukka a 2024.

A cewarsa, adadin mutum 30,313 wadanda ake zargi da manyan laifuka ne aka kama, yayin da kuma aka kwato motocin sata guda 1,438 a hannun ‘yan ta’addan cikin 2024.

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Ya kuma kara da cewa yunkurin jami’an tsaron a 2024 ya kai ga dakile satar mai da darajarsa ya kai naira biliyan 57 da kuma taimakawa wajen tabbatar da samun nasarar kara hako mai zuwa ganga miliyan 1.8 a kowace rana.

Mijinyawa ya ce, bisa burin fadar shugaban kasa an samu nasarar rage satar danyen mai a yankin Neja Delta.

Ya kuma ce hukumar kula da gyaran tarbiyya (NCoS) ta tsare da kare mutunci da kimar fursunonin 80,000 tare da kula da masu laifukan 50,000. Ya kara da cewa an horas da fursunoni sama da 30,000 sana’o’in hannu, fursunoni 2,000 sun zana jarabawar kammala sakandari, yayin da wasu 1,000 suka kammala karatun diploma da digiri a jami’ar karatu daga gida (NOUN).

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
Manyan Labarai

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
Manyan Labarai

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Next Post
Da Rancen Naira Tiriliyan 13 Za A Cike Gibin Kasafin Kudin 2025 — Edun

Da Rancen Naira Tiriliyan 13 Za A Cike Gibin Kasafin Kudin 2025 — Edun

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.