• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rushewar Gini Ya Kashe Rayuka 4, An Ceto Mutane 105 A Abuja A 2024 – FEMD

by Abubakar Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Rushewar Gini Ya Kashe Rayuka 4, An Ceto Mutane 105 A Abuja A 2024 – FEMD
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

Ma’aikatar bayar da qgajin gaggawa ta babban birnin tarayya (FEMD) ta bayyana cewa an ceto mutane 105, yayin da rayuka huɗu suka salwanta sakamakon jerin hadɗarurrukan rushewar gine-gine a fadin birnin tarayya a shekarar 2024.

Muƙaddashin daraktan FEMD, Injiniya Abdulrahman Mohammed, ya bayyana wannan a taron manema labarai da aka gudanar ranar Litinin a Abuja. Ya bayyana cewa rushewar gine-ginen ya faru a unguwannin Prince and Princess Estate, da Guzape District, da Garki 2, da Kubwa, da Sabon Lugbe kusa da hanyar tashar jirgin sama.

  • Mutum 10 Sun Mutu A Turmutsutsin Rabon Shinkafa A Abuja
  • Wike Ya Bai Wa Asibitocin Gwamnati Umarnin Tallafa Wa Wadanda Turmutsitsin Abuja Ya Rutsa

Mohammed ya ƙara da cewa FEMD ta fuskanci manyan matsalolin da suke buƙatar taimakon gaggawa a wannan shekarar, ciki har da rushewar gine-gine, da gobara, da ambaliyar ruwa, da girgizar kasa, da rabon kayan tallafi ga waɗanda abin ya shafa. Ya ce a cikin shekarar, an ceto mutane kimanin 3,500 daga yanayi daban-daban na gaggawa, tare da amsa kiran gaggawa 165 ta layin wayar su mai sauƙin kira, 112.

Ya kuma bayyana cewa FEMD ta fara amfani da fasahar zamani wajen inganta tsarin gudanar da agaji. Wannan yana ƙunshe da amfani da tauraron ɗan Adam mai zagaya ƙasa don samun hotuna da bayanai na zahiri da za su taimaka wajen tantance haɗurruka da rage matsaloli a birnin tarayya. Mohammed ya yi kira da a ƙara amfani da sabbin dabaru don magance matsalolin da ake fuskanta a cikin birnin nan gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abuja
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yankunan Arewacin Kasar Sin Na Taka Rawar Gani Wajen Kare Filayen Noma

Next Post

Matsakaita Da Kananan Kamfanonin Sin Na Nuna Himma Da Gwazo Wajen Yin Kirkire-Kirkire

Related

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto
Labarai

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

7 hours ago
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

11 hours ago
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

12 hours ago
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
Labarai

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

13 hours ago
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

15 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

18 hours ago
Next Post
Matsakaita Da Kananan Kamfanonin Sin Na Nuna Himma Da Gwazo Wajen Yin Kirkire-Kirkire

Matsakaita Da Kananan Kamfanonin Sin Na Nuna Himma Da Gwazo Wajen Yin Kirkire-Kirkire

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.