• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Rabar Da Naira Biliyan 16.1 Ga Masana’antu 22 — Ministan Kudi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Ta Rabar Da Naira Biliyan 16.1 Ga Masana’antu 22 — Ministan Kudi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayyar ta ce, ta rabar da zunzurutun kudade har naira biliyan 16.1 ga masana’antu su 22 da suka kamata daga cikin naira biliyan 75 da gwamnatin ta ware domin ingantawa da bunkasa bangaren.

Kazalika, ta kuma ce a cikin kwana biyar kacal ta rabar da wani karin naira biliyan 3.5 ga wadanda suka ci gajiya su 11,000 daga tsarin tura kudi ga masu bukata ‘Consumer Credit Scheme’, wanda ke da burin cimma ‘yan Nijeriya miliyan 80 domin agaza musu.

Gwamnatin tarayya ta ce mutane miliyan 25 zuwa yanzu suka amfana da tsarin tura kudin kai tsaye ga masu cin gajiya.

Wannan bayanan sun fito ne daga bakin ministan kudi da tsare-tsaren tattalin arziki, Wale Edun, wanda ya bayyana a Abuja yayin taron ‘yan kasa da masu ruwa da tsaki kan aiwatar da manufofin da shugaban kasa da ministoci suka gabatar a zangon karshe na 2024.

Ya ce, Nijeriya na bukatar zuba hannun jari na akalla dala biliyan 20 kowace shekara domin samun nasarar zuwa ga muradin inganta tattalin arziki da samun damar inganta matakin ci gaba zuwa kaso 6.3 nan da shekarar 2027.

Labarai Masu Nasaba

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Da yake sake nanata bukatar zuba hannun jari cikin gaggawa, Mista Edun ya shelanta irin tasirin da zuba hannun jari ke da shi ga jagorantar ci gaban tattalin arziki da bunkasarsa hadi da taimakawa wajen aiwatar da ayyukan raya kasa.

Edun ya ce, “A zahirin gaskiya muna matukar bukatar karin ci gaba. Samun karin dala biliyan 20 duk shekara shi ne burin da muke da shi don samar da ababen more rayuwa da kuma samar da kayan aikin noma.”

Bugu da kari, Edun ya danganta tsarin kasafin kudi da daidaiton farashin musayar kudade su ne za su taimaka wa Nijeriya ta samu janyo hankalin masu zuba hannun jari sosai.

Kazalika, ministan kudin ya ce akwai gayar bukatar amincewa da sabon kudirin garambawul ga haraji, wanda ya bai wa ‘yan Nijeriya tabbacin cewa za su amfana daga wannan kudirin gyaran harajin.

Ya roki ‘yan majalisun kasa da su toshe kunnuwansu kawai su amince da kudirin domin amfanunsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gombe Ta Kafa Tarihi Na Amincewa Da Dokar Kare Masu Bukata Ta Musamman

Next Post

Sojoji Za Su Tabbatar Da Manoma Kashi 85 Sun Yi Noma Lafiya A Damina Mai Zuwa – Sanata Yari

Related

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

8 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

9 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

9 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

10 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

13 hours ago
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
Labarai

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

13 hours ago
Next Post
Sojoji Za Su Tabbatar Da Manoma Kashi 85 Sun Yi Noma Lafiya A Damina Mai Zuwa – Sanata Yari

Sojoji Za Su Tabbatar Da Manoma Kashi 85 Sun Yi Noma Lafiya A Damina Mai Zuwa - Sanata Yari

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.