• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ACF Ta Nemi Rundunar Soji Ta Sake Dabarun Yakinta, Bayan Luguden Wutar Silame

by Khalid Idris Doya
8 months ago
in Labarai
0
ACF Ta Nemi Rundunar Soji Ta Sake Dabarun Yakinta, Bayan Luguden Wutar Silame
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Dattawan Arewa (ACF), ta bukaci sojojin Nijeriya da su sake duba dabarbaru da hikimomin da suke bi wajen magance matsalolin tsaro a arewacin kasar da ma Nijeriya baki daya.

A wata sanarwar da jami’in watsa labarai na kungiyar, Farfesa Tukur Muhammad Baba, ya fitar a ranar Litinin, ACF ta nuna damuwarta kan yadda ake samun ‘yan kura-kurai a aikace-aikacen sojojin.

Kungiyar ta nuna takaici kan yadda jirgin yakin sojoji ya yi luguden wuta a wasu kauyuka biyu a karamar hukumar Silame a Jihar Sakkwato a ranar Laraba, 25 ga watan Disamban 2024.

Harin wanda ya janyo mutuwar fafaren hula goma da jikkata wasu da dama.

Kungiyar Dattawan Arewan ta yaba wa gwamantin tarayya da gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmed Aliyu bisa hanzarin kai dauki da daukan nauyin jinyar wadanda suka raunata tare da bata wani lokaci ba.

Labarai Masu Nasaba

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

“ACF ta kadu sosai da wannan lamarin na Silame, abun ya yi yawa a kasar nan. Irin wannan harin ya faru a kauyen Tudun Biri da ke Jihar Kaduna da Jihar Adamawa da Nasarawa, da jikkata mutane da dama wanda har yanzu muna fama da wadannan radadin a zukatanmu.”

A cewarsa sanarwar, kungiyar a kowani lokaci tana karfafa gwiwar hukumomin tsaro wajen yaki da kowace nauyin ta’addanci a fadin kasar nan, amma ba hakan ba ne zai ba su damar kashe fafaren hula ba tare da sun ji ko sun gani ba.

“Babu wanda ya isa ya shiga shakku game da irin wannan goyon bayan namu, kuma ACF ta yi kira ga duk wani mai kishin kasa a Nijeriya da ya ba jami’an tsaro goyon baya. Abu ne kawai da ba za a yarda da shi ba a bar ‘yan ta’adda da masu aikata laifuka na kowane irin launi su rike al’umma don neman kudin fansa ta hanyar ayyukansu na kiyayya.

“Wannan, abubuwan da suka faru irinsu na Silame da sauran wadanda suka faru kafin shi da kuma kididdigar tasirinsu ga ‘yan kasa marasa laifi suna daukar wani tsari mafi tayar da hankali tare da asarar Dan’adam wanda ba za a yarda da shi ba.”

Daga bisani kungiyar ta yi kira ga sojojin da su maida hankali wajen gudanar da ayyukansu bisa kwarewa da sanin ya kamata domin kauce wa faruwar irin wannan lamarin a nan gaba ta hanyar duba dabarun da hikimomin yaki da suke yi wajen kai farmakisu ga ‘yan ta’adda.

Kungiyar Dattawan Arewan ta kuma nemi masu hannu da shuni da kungiyoyi da su kai agaji da tallafi ga wadanda lamarin ya shafa domin rage musu radadin halin da suke ciki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Arewa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Ta Karɓi Bashin Dala Biliyan 1.5 Daga Bankin Duniya Bayan Cire Tallafin Mai

Next Post

Manyan Batutuwa 10 Da Suka Mamaye Siyasar Nijeriya A 2024

Related

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

3 hours ago
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara
Labarai

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

4 hours ago
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu
Labarai

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

5 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

6 hours ago
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

6 hours ago
Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba
Labarai

Yara 400,000 Ne Ke Kamuwa Da Cutar Kansa Duk Shekara A Duniya

6 hours ago
Next Post
Manyan Batutuwa 10 Da Suka Mamaye Siyasar Nijeriya A 2024

Manyan Batutuwa 10 Da Suka Mamaye Siyasar Nijeriya A 2024

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 5, 2025
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.