ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ACF Ta Nemi Rundunar Soji Ta Sake Dabarun Yakinta, Bayan Luguden Wutar Silame

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Acf

Kungiyar Dattawan Arewa (ACF), ta bukaci sojojin Nijeriya da su sake duba dabarbaru da hikimomin da suke bi wajen magance matsalolin tsaro a arewacin kasar da ma Nijeriya baki daya.

A wata sanarwar da jami’in watsa labarai na kungiyar, Farfesa Tukur Muhammad Baba, ya fitar a ranar Litinin, ACF ta nuna damuwarta kan yadda ake samun ‘yan kura-kurai a aikace-aikacen sojojin.

Kungiyar ta nuna takaici kan yadda jirgin yakin sojoji ya yi luguden wuta a wasu kauyuka biyu a karamar hukumar Silame a Jihar Sakkwato a ranar Laraba, 25 ga watan Disamban 2024.

ADVERTISEMENT

Harin wanda ya janyo mutuwar fafaren hula goma da jikkata wasu da dama.

Kungiyar Dattawan Arewan ta yaba wa gwamantin tarayya da gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmed Aliyu bisa hanzarin kai dauki da daukan nauyin jinyar wadanda suka raunata tare da bata wani lokaci ba.

LABARAI MASU NASABA

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

“ACF ta kadu sosai da wannan lamarin na Silame, abun ya yi yawa a kasar nan. Irin wannan harin ya faru a kauyen Tudun Biri da ke Jihar Kaduna da Jihar Adamawa da Nasarawa, da jikkata mutane da dama wanda har yanzu muna fama da wadannan radadin a zukatanmu.”

A cewarsa sanarwar, kungiyar a kowani lokaci tana karfafa gwiwar hukumomin tsaro wajen yaki da kowace nauyin ta’addanci a fadin kasar nan, amma ba hakan ba ne zai ba su damar kashe fafaren hula ba tare da sun ji ko sun gani ba.

“Babu wanda ya isa ya shiga shakku game da irin wannan goyon bayan namu, kuma ACF ta yi kira ga duk wani mai kishin kasa a Nijeriya da ya ba jami’an tsaro goyon baya. Abu ne kawai da ba za a yarda da shi ba a bar ‘yan ta’adda da masu aikata laifuka na kowane irin launi su rike al’umma don neman kudin fansa ta hanyar ayyukansu na kiyayya.

“Wannan, abubuwan da suka faru irinsu na Silame da sauran wadanda suka faru kafin shi da kuma kididdigar tasirinsu ga ‘yan kasa marasa laifi suna daukar wani tsari mafi tayar da hankali tare da asarar Dan’adam wanda ba za a yarda da shi ba.”

Daga bisani kungiyar ta yi kira ga sojojin da su maida hankali wajen gudanar da ayyukansu bisa kwarewa da sanin ya kamata domin kauce wa faruwar irin wannan lamarin a nan gaba ta hanyar duba dabarun da hikimomin yaki da suke yi wajen kai farmakisu ga ‘yan ta’adda.

Kungiyar Dattawan Arewan ta kuma nemi masu hannu da shuni da kungiyoyi da su kai agaji da tallafi ga wadanda lamarin ya shafa domin rage musu radadin halin da suke ciki.

Acf
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa
Da ɗumi-ɗuminsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa
Manyan Labarai

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia
Labarai

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026
Next Post
Manyan Batutuwa 10 Da Suka Mamaye Siyasar Nijeriya A 2024

Manyan Batutuwa 10 Da Suka Mamaye Siyasar Nijeriya A 2024

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

July 10, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

July 10, 2026
CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

July 10, 2026
Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

July 10, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?

July 10, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.