• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar ‘J5 Container’ Ta Gudanar Da Taron Neman Hadin Kan Jami’an Tsaro A Legas

by Bala Kukuru
5 months ago
in Labarai
0
Kungiyar ‘J5 Container’ Ta Gudanar Da Taron Neman Hadin Kan Jami’an Tsaro A Legas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Alhamis ce, Kungiyar NURTW ta kasa bangaren ‘J5 container’ reshan Jihar Legas a shiyar kasuwar Mile12 Intanashinal maket karkashin jagorancin shugabanta, Alhaji Umar Ahmed Isah ta gudanar da taron neman hadin kan jami’an tsaro na bangarori daban-daban na cikin garin Legas.

Kungiyar ta hada kai ne da bangarorin jami’an tsaro da suka hada da hukumar Kwaston da hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA) da hukumar kula da hanyoyi da hukumar ‘yansanda da dai sauransu.

  • Tinubu Ya Isa Legas Don Gudanar Da Bukukuwan Kirsimeti Da Sabuwar Shekara 
  • Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Legas Za Ta Kara Samar Da Kwararru – Kwamishina

Taron neman hadin kan jami’an tsaron ya samu halartar dukkan wakilan kungiyar na kananan hukumomin Jihar Legas da shugabanta na wasu jihohin arewacin Nijeriya, wanda suka hada da shugaban kungiyar na Kaduna, Suleman Muhammad Kaduna da shugaban kungiyar na Kano, Muhammad Sani Kano da shugaban kungiyar na Katsina, Idiris Umar Katsina da shugaban kungiyar na Filato, Kwamared Isah Filato da shugaban kungiyar Narto na Filato, Buhari Bulama.

Sauran sun hada da shugaban kungiyar na Bauchi, Buhari Suleman Bauchi da shugaban kungiyar na Borno, Ahmed Muhammad Barno da shugaban kungiyar Nato a Abuja, Umar Sarki da shugaban kungiyar na Kafanchan, Maiwada Musa da ko’odinetan kungiyar a Jos, Salisu Adamu da sauran shugaban kasuwar Mile12 Intanashinal maket, Alhaji shehu Usman Jibirin.

Makasudin gudanar da wannan shi ne, neman hadin kan jami’an tsaro da kuma jaddada dankon zumunci a tsakaninsu tare da kara fahimtar juna baki daya, a yayin da jami’an tsaron na kowanne bangare suka gabatar da jawabansu daya bayan daya tare da jawo hankulan direbobin da su daina shan kwayoyi da kuma rage yin gudu a lokacin da suke tuki, domin kare lafiyarsu da rayuwar fasinjojinsu.

Labarai Masu Nasaba

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Haka kuma sun shawarci direbobin J5 container da sauran direbobi masu daukar kaya daga Legas zuwa arewacin Nijeriya da su rika tantance kayan da za su dauka kafin a loda masu a motocinsu, domin kauce wa daukar haramtaccen kayan da gwamnati ba ta yarda da shi ba.

Shugaban kungiyar J5 container da ke shiyar kasuwar Mile 12, Alhaji Umar Ahmed Isah ya yi jawabin godiya ga shugaban kungiyar na kasa da wakilanta na jihohi dangane da irin gudummawar da suke bai wa kungiyar NURTW tun daga sama har zuwa kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Legas
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Karrama Kwamishinan Ma’aikatar Ayyuka Na Katsina A Matsayin Mafi Kwazo

Next Post

Sakataren Gwamnatin Ondo Ya Rasu Bayan Hatsarin Mota

Related

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

58 minutes ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

5 hours ago
J5
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

6 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

7 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

10 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

13 hours ago
Next Post
Sakataren Gwamnatin Ondo Ya Rasu Bayan Hatsarin Mota

Sakataren Gwamnatin Ondo Ya Rasu Bayan Hatsarin Mota

LABARAI MASU NASABA

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
J5

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.