• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar ‘J5 Container’ Ta Gudanar Da Taron Neman Hadin Kan Jami’an Tsaro A Legas

by Bala Kukuru
8 months ago
in Labarai
0
Kungiyar ‘J5 Container’ Ta Gudanar Da Taron Neman Hadin Kan Jami’an Tsaro A Legas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Alhamis ce, Kungiyar NURTW ta kasa bangaren ‘J5 container’ reshan Jihar Legas a shiyar kasuwar Mile12 Intanashinal maket karkashin jagorancin shugabanta, Alhaji Umar Ahmed Isah ta gudanar da taron neman hadin kan jami’an tsaro na bangarori daban-daban na cikin garin Legas.

Kungiyar ta hada kai ne da bangarorin jami’an tsaro da suka hada da hukumar Kwaston da hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA) da hukumar kula da hanyoyi da hukumar ‘yansanda da dai sauransu.

  • Tinubu Ya Isa Legas Don Gudanar Da Bukukuwan Kirsimeti Da Sabuwar Shekara 
  • Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Legas Za Ta Kara Samar Da Kwararru – Kwamishina

Taron neman hadin kan jami’an tsaron ya samu halartar dukkan wakilan kungiyar na kananan hukumomin Jihar Legas da shugabanta na wasu jihohin arewacin Nijeriya, wanda suka hada da shugaban kungiyar na Kaduna, Suleman Muhammad Kaduna da shugaban kungiyar na Kano, Muhammad Sani Kano da shugaban kungiyar na Katsina, Idiris Umar Katsina da shugaban kungiyar na Filato, Kwamared Isah Filato da shugaban kungiyar Narto na Filato, Buhari Bulama.

Sauran sun hada da shugaban kungiyar na Bauchi, Buhari Suleman Bauchi da shugaban kungiyar na Borno, Ahmed Muhammad Barno da shugaban kungiyar Nato a Abuja, Umar Sarki da shugaban kungiyar na Kafanchan, Maiwada Musa da ko’odinetan kungiyar a Jos, Salisu Adamu da sauran shugaban kasuwar Mile12 Intanashinal maket, Alhaji shehu Usman Jibirin.

Makasudin gudanar da wannan shi ne, neman hadin kan jami’an tsaro da kuma jaddada dankon zumunci a tsakaninsu tare da kara fahimtar juna baki daya, a yayin da jami’an tsaron na kowanne bangare suka gabatar da jawabansu daya bayan daya tare da jawo hankulan direbobin da su daina shan kwayoyi da kuma rage yin gudu a lokacin da suke tuki, domin kare lafiyarsu da rayuwar fasinjojinsu.

Labarai Masu Nasaba

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

Haka kuma sun shawarci direbobin J5 container da sauran direbobi masu daukar kaya daga Legas zuwa arewacin Nijeriya da su rika tantance kayan da za su dauka kafin a loda masu a motocinsu, domin kauce wa daukar haramtaccen kayan da gwamnati ba ta yarda da shi ba.

Shugaban kungiyar J5 container da ke shiyar kasuwar Mile 12, Alhaji Umar Ahmed Isah ya yi jawabin godiya ga shugaban kungiyar na kasa da wakilanta na jihohi dangane da irin gudummawar da suke bai wa kungiyar NURTW tun daga sama har zuwa kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Legas
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Karrama Kwamishinan Ma’aikatar Ayyuka Na Katsina A Matsayin Mafi Kwazo

Next Post

Sakataren Gwamnatin Ondo Ya Rasu Bayan Hatsarin Mota

Related

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

2 seconds ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

1 hour ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

4 hours ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

5 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

5 hours ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

6 hours ago
Next Post
Sakataren Gwamnatin Ondo Ya Rasu Bayan Hatsarin Mota

Sakataren Gwamnatin Ondo Ya Rasu Bayan Hatsarin Mota

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.