ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar ‘J5 Container’ Ta Gudanar Da Taron Neman Hadin Kan Jami’an Tsaro A Legas

by Bala Kukuru
1 year ago
J5

A ranar Alhamis ce, Kungiyar NURTW ta kasa bangaren ‘J5 container’ reshan Jihar Legas a shiyar kasuwar Mile12 Intanashinal maket karkashin jagorancin shugabanta, Alhaji Umar Ahmed Isah ta gudanar da taron neman hadin kan jami’an tsaro na bangarori daban-daban na cikin garin Legas.

Kungiyar ta hada kai ne da bangarorin jami’an tsaro da suka hada da hukumar Kwaston da hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA) da hukumar kula da hanyoyi da hukumar ‘yansanda da dai sauransu.

  • Tinubu Ya Isa Legas Don Gudanar Da Bukukuwan Kirsimeti Da Sabuwar Shekara 
  • Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Legas Za Ta Kara Samar Da Kwararru – Kwamishina

Taron neman hadin kan jami’an tsaron ya samu halartar dukkan wakilan kungiyar na kananan hukumomin Jihar Legas da shugabanta na wasu jihohin arewacin Nijeriya, wanda suka hada da shugaban kungiyar na Kaduna, Suleman Muhammad Kaduna da shugaban kungiyar na Kano, Muhammad Sani Kano da shugaban kungiyar na Katsina, Idiris Umar Katsina da shugaban kungiyar na Filato, Kwamared Isah Filato da shugaban kungiyar Narto na Filato, Buhari Bulama.

ADVERTISEMENT

Sauran sun hada da shugaban kungiyar na Bauchi, Buhari Suleman Bauchi da shugaban kungiyar na Borno, Ahmed Muhammad Barno da shugaban kungiyar Nato a Abuja, Umar Sarki da shugaban kungiyar na Kafanchan, Maiwada Musa da ko’odinetan kungiyar a Jos, Salisu Adamu da sauran shugaban kasuwar Mile12 Intanashinal maket, Alhaji shehu Usman Jibirin.

Makasudin gudanar da wannan shi ne, neman hadin kan jami’an tsaro da kuma jaddada dankon zumunci a tsakaninsu tare da kara fahimtar juna baki daya, a yayin da jami’an tsaron na kowanne bangare suka gabatar da jawabansu daya bayan daya tare da jawo hankulan direbobin da su daina shan kwayoyi da kuma rage yin gudu a lokacin da suke tuki, domin kare lafiyarsu da rayuwar fasinjojinsu.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Haka kuma sun shawarci direbobin J5 container da sauran direbobi masu daukar kaya daga Legas zuwa arewacin Nijeriya da su rika tantance kayan da za su dauka kafin a loda masu a motocinsu, domin kauce wa daukar haramtaccen kayan da gwamnati ba ta yarda da shi ba.

Shugaban kungiyar J5 container da ke shiyar kasuwar Mile 12, Alhaji Umar Ahmed Isah ya yi jawabin godiya ga shugaban kungiyar na kasa da wakilanta na jihohi dangane da irin gudummawar da suke bai wa kungiyar NURTW tun daga sama har zuwa kasa.

J5
Bala Kukuru
+ postsBio
  • Bala Kukuru
    https://hausa.leadership.ng/author/bala-kukuru/
    Yadda Tashin Farashin Man Fetur Ya Shafi Harkokin Kasuwanci A Nijeriya
  • Bala Kukuru
    https://hausa.leadership.ng/author/bala-kukuru/
    Dan Majlisa Ya Tallafa Wa Al’ummar Mazabarsa Da Kayan Abinci Na Naira Miliyan 45 A Katsina
  • Bala Kukuru
    https://hausa.leadership.ng/author/bala-kukuru/
    Alhaji Amadu Umar Ya Zama Sarkin Hausawan Garin Agbara A Jihar Ogun
  • Bala Kukuru
    https://hausa.leadership.ng/author/bala-kukuru/
    Sana’ar Safarar Dabbobi A Halin Yanzu Sai Godiya -Aminu Isimaila

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Sakataren Gwamnatin Ondo Ya Rasu Bayan Hatsarin Mota

Sakataren Gwamnatin Ondo Ya Rasu Bayan Hatsarin Mota

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.