• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NPA Ta Buƙaci A Yi Nazari Kan Tsarin Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa Na Ƙasa Da Ƙasa

by Bello Hamza
8 months ago
in Labarai
0
NPA Ta Buƙaci A Yi Nazari Kan Tsarin Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa Na Ƙasa Da Ƙasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manajin Darakta na Hukumar Tashar Jirgin Ruwa ta Kasa NPA, Dakta Abubakar Dantsoho, ya bukaci da a yi nazari kan wanzar da tsarin tashoshin Jiragen Ruwa kasa da kasa da samar da kayan tabbatar da tsaro ISPS, musamman domin a kara samarwa da fannin tsaron da ya kamata.

Abubakar ya yi wannan kiran ne, a jawabinsa a taron kasa na 2024 da kungiyar jami’an ma’aikata a Tashoshin Jirage Ruwa ta kasa wato SOFN.

  • Harajin “VAT” Zai Kara Wa Al’ummar Kasar Nan Kuncin Rayuwa Ne Kawai – Gambo Danpass
  • An Jinjina Wa Tawagar NPA Kan Samun Nasarar Sayar Da Danyen Mai Da Takardar Naira

Ya yi nuni da cewa, yin nazarin zai tabbatar da samar da wadataccen tsaro, musamman ta hanyar samar da kayan zamani na wanzar da tsaro, a daukacin tashoshin Jiragen Ruwa na kasar.

“A yayin da muke yin dubi da shekarun baya, ya kamata mu san gudunmawar da samar da tsaro ke bayawa a tekunan kasar nan, musamman domin a samu damar gudanar da hada-hadar kasuwanci na kasa da kasa tare da kuma tabbatar da, ana samar da kariya ga direbon Jiragen ruwa da kuma ma’aikatan da ke aiki a tashoshin Jiragen ruwa, “ inji shi.

Ya sanar da tsarin na ISPS Code wanda ya fara aiki gadan-gadan 2004, zai taimaka wajen kara samar da tsaro a tashoshin Jiragen ruwan kasar da kuma dakile dukkan wata barazana ta rashin tsaro a fannin.

Labarai Masu Nasaba

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

A cewarsa, “Ga Nijeriya, tamkar kira ne na fara zuba hannun jari domin a kara habaka tsarin, wanda bai kawai bayar da kariya ga tashoshin Jiragen ruwan kasar ba, amma a kara kare martabar kasar mu, wacce take ita ce, uwa maba da mama, ga sauran kasashen da ke a cikin Afirka.

Ya sanar da cewa, shirye-shiyen wanzar da tsarin na ISPS Code 2020 a duniya, ya fuskance kalubale wanda suka hada da; ayyukan ta’addanci, ‘yan fashin teku, safarar haramtattun kaya da sauransu

Sai dai, Dantsoho ya sanar da cewa, yanu duniya na sauya wa ne, wanda hakan ya sanya hukumar ta NPA, ta gay a kamata ta rungumi tsarin na ISPS Code, tare da kuma wanzar dashi, gadan-gadan.

Dantsoho ya ci gaba da cewa, a namu bangaren a hukumar, muna bukatar sama da sauyi, wanda hakan ya sanya muka sabunta kayan aiki, musamman samar da kayan aiki na kimiyyar zamani, ana kuma kara samun masu zuba hannun jari da horar da jami’an tsaron mu, domin dakile dauk wata barazana da za ta iya kunno kai.

Ya sanar da cewa, hukumar tare da  hukumomin Gwamnatin Tarayya da na jihohi, masu kula da kayan aiki a tashoshin Jiragen ruwan kasar da kuma aboan hadakar mu na kasa da kasa, suna gudanar da aiki, kafada da kafada domin kara tabbatar da tsaro a fannin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwarinpa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manyan Batutuwa 10 Da Suka Mamaye Siyasar Nijeriya A 2024

Next Post

Alhaji Amadu Umar Ya Zama Sarkin Hausawan Garin Agbara A Jihar Ogun

Related

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

6 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

12 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

13 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

14 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

15 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

16 hours ago
Next Post
Alhaji Amadu Umar Ya Zama Sarkin Hausawan Garin Agbara A Jihar Ogun

Alhaji Amadu Umar Ya Zama Sarkin Hausawan Garin Agbara A Jihar Ogun

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.