ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Jinjina Wa Tawagar NPA Kan Samun Nasarar Sayar Da Danyen Mai Da Takardar Naira

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 years ago
Gaza

Shugaban Karamin Kwamitin Fasaha na wanzar da tsarin Gwamnatin Tarayya na dayen mai da ake sayarwa na cikin gida da kayan da ake sarrafawa a kan takardar Naira Zacch Adedeji, ya jinjiawa tawagar shirin sayen kaya wato (OSS) wadda Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, ke jagorantar tabbatar an gudanar da ayyukan a cikin nasara.

Adedeji wanda kuma shi ne, Shugaban Hukumar tara Haraji ta kasa ya ya yi wannan yabon ne, a lokacin da ya kai ziyarar aiki a shalkawatar Hukumar NPA a ranar Alhamis da ta gabata.

  • Zargin China Da Bautar Da Leburori a Gonar Tumatir a Xinjiang: Mene Ne Gaskiyar Lamarin?
  • Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda A Zamfara

Kazalika, Adedeji, ya godewa, tawagar ta Hukumar NPA, kan irin gudunmawar da take bayarwa wajen wanzar da umarnin na fadara shugaban kasa na ayyukan sayar da danyen man a cikin gida Nijeriya da kuma sauran kayan da ake sararafwa kan takardar Naira

ADVERTISEMENT

Adedeji ya kara da cewa,“Mun lura da namijin kokarin da tawagar ke kan yi wajen samun nasarar gudanar da ayyukan, wanda hakan ya kuma nuna irin kishin kasar da tawagar take da shi, na son cimma nasara”.

Ya ci gaba da cewa,“ A saboda haka, muna karawa tawagar kwarin guiwar da su kara zagewa da kuma mayar da hankali domin a samu cimma nasarar gudanar da shirin.”

LABARAI MASU NASABA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

Adedeji ya ce,“ Muna mika godiyar mu ga sauran hukumomi da suke a cikin wannan aikin, saboda irin dimbin goyon baya da hadin kai da suka bayarwa”.

Da yake mayar da na sa bayanin, Babban Manajin Darakta na Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, Dakta Abubakar Dantsoho ya bayyana cewa, “ Wannan yabon da Kwamitin ya yiwa tawagar, zai karawa tawagar kwarin guiwa ne, wajen kara mayar da hankali kan shirin”.

Dakta Dantsoho ya kuma yi amfani da damar wajen yabawa ministan Tattalin Arziki na Albarkatun Ruwa Hon. Adegboyega Oyetola a kan samar da sahihin shuganaci na gari, wanda hakan ya taimaka, wajen samun cin nasarar shirin.

“Muna godewa namjin kokarin Shugaban Karamin Kwamitin Zacch Adedeji, musamman kan goyon bayan da yake bayarwa har ta kai ga, shirin ya samu cimma wannan nasarar”.

Kazalika, Dakta Dantsoho, ya bayya cewa, bisa samar da wannan shirin, na sayar da danyen man kan takardar Naira da kuma kayan da ake sarrafawa a cikin Nijeriya, hakan ya nuna yadda Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya taimaka wajen ragewa Nijeriya yin asarar biliyoyin Naira.

Dakta Dantsoho ya kara da cewa, hakan ya kuma bayar da wata dama na kula da fannin makamashi na kasar, kara zurafafa cinikayya, samar da ayyukan yi ga ‘yan Nijeriya, damar rage karancin albarkatun man fetur da kuma kawo karashen jerin Gwanonin layukan ababen hawa a gidajen sayar da man fetur na kasar, musamman a wannan lokutan na bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara.

Wannan shirin dai na zuwa ne, daidai lokacin da matatar man fetur ta Dangote, ta rage farashin man da take samarwa samfarin PMS zuwa Naira 899.50 na kowacce lita daya,

Sauran tawagar da ke a cikin Kwamtin sun hada da Hukumomin NIMASA, NMDPRA, NUPRC, NEPZA, FIRS, NNPC, DAPMAN, IPMAN, PHS, MEMAN, NDLEA, Matatar Dangote, Kwantirola na Kwastam da kuma Hafsan Rundunar Sojin Sama.

Npa
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Npa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas
Tattalin Arziki

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

September 4, 2026
NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
Tattalin Arziki

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

September 4, 2026
NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja
Tattalin Arziki

NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja

August 28, 2026
Next Post
Manyan Bankunan Kasa Na Sin Da Nijeriya Sun Sabunta Yarjejeniyar Musayar Kudi

Manyan Bankunan Kasa Na Sin Da Nijeriya Sun Sabunta Yarjejeniyar Musayar Kudi

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.