• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Binciki Tashin Rikicin Addini A Kudu Maso Yamma

by Khalid Idris Doya
8 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Za Ta Binciki Tashin Rikicin Addini A Kudu Maso Yamma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da yiyuwar gwamnatin tarayya za ta aiwatar da wani bincike na musamman kan wasu harkokin addinai da ke haifar da tashin-tashina na addini a wasu sassan kudu maso yammacin kasar.

A wani binciken da majiyarmu ta gudanar, ya tabbatar mata da cewa gwamnatin tarayya ta nuna damuwarta matuka kan rahotonnin aikace-aikacen da ake samu na wasu kungiyoyin masu tsattsaurar ra’ayi da tashin hankali na addini.

  • Bajintar Aiki: Majalisar Dattawa Ta Jinjina Wa Ministan YaÉ—a Labarai
  • Yakin Haraji Da Gwamnatin Amurka Ke Gudanarwa Na Jefa Fargaba a Zukatan Amurkawa

A baya-bayan nan wasu lamura biyu sun wakana a Jihar Oyo wanda ake zargin masu tsattsaurar ra’ayi ne suka haifar da ke tasiri a shiyyar kudu maso yamma, wanda kai tsaye aka fahimci ka iya janyo tashin hankali mai tsauri na addini.

Majiyoyi masu tushe sun tabbatar da cewa an sanar da hukumomin tsaro wadannan aikace-aikacen da ake zargin na masu tsautsaurar ra’ayin ne a kudu maso yammacin kasar domin neman daukan matakan gaggawa.

Majiyoyin sun ce tunin aka bayar da umurni ga jami’an tsaro da su bi sawun lamarin a sirrance domin kawo karshen matsalar tun kafin ta yi kamari.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

Wata majiya ta ce baya ga barazanar kungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi da ‘yan ta’adda da ke kokarin kutsawa yankin ta tsohon gandun dajin Oyo da dajin Kamoko, wanda ya taso daga jihohin Kaduna da Neja da Kwara da kuma dajin Oyo, akwai rahotannin da ke cewa, wasu kungiyoyi masu tsattsauran ra’ayi suma suna yunkurin shiga yankin Kudu maso Yamma da yada kiyayya ta addini.

An kuma gano cewa jami’an tsaron sun fara binciken wata kungiyar da ke yunkuri kan shari’a wacce a baya-bayan nan ta yi barazanar kafa kotun shari’a a cikin Oyo. Majiyoyin sun ce makonnin da suka gabata jami’an tsaro sun yi tambayoyi ta mutane da dama da suke da alaka da shirin kafa shari’a a Oyo.

Haka kuma an gano cewa yunkurin masu shari’a shi ne don su kafa majalisar shari’a da za ta kula da wasu harkokin jama’a kamar aure, sakin aure da gado, saboda sun fahimci kotunan da ke akwai a halin yanzu sun aminta ne da harkokin kwansitushin.

A halin da ake ciki kuma, jam’iyyar ‘Oodua People’s Congress’ (OPC) karkashin Fredrick Fasheun, ta bukaci daukacin gwamnonin Kudu maso Yamma shida da su dauki matakin gaggawa na tsaro wajen tarwatsa sansanonin ‘yan ta’adda da ke fitowa daga Arewa, a cikin dazuzzukan Yarbawa, tare da yin alkawarin taimaka wa jami’an tsaro wajen magance matsalar barazanar ba tare da bata lokaci ba kafin a makara.

OPC a wata sanarwar da ta fitar, ta ce, a shirye take kuma akwai zaratan da za su taimaka wa jami’an tsaro wajen kawo karshen wadanda ake zargin ‘yan ta’adda ne da suke kwararowa daga arewa zuwa kudu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BincikeGwamnatin Tarayyarikicin Addini
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Mai Bude Kofarta Na Maraba Da Cudanyar Al’ummun Duniya

Next Post

Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Donald Trump

Related

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

2 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

4 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

5 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

6 hours ago
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja
Labarai

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

8 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

9 hours ago
Next Post
Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Donald Trump

Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Donald Trump

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.