ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Binciki Tashin Rikicin Addini A Kudu Maso Yamma

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Addini

Da yiyuwar gwamnatin tarayya za ta aiwatar da wani bincike na musamman kan wasu harkokin addinai da ke haifar da tashin-tashina na addini a wasu sassan kudu maso yammacin kasar.

A wani binciken da majiyarmu ta gudanar, ya tabbatar mata da cewa gwamnatin tarayya ta nuna damuwarta matuka kan rahotonnin aikace-aikacen da ake samu na wasu kungiyoyin masu tsattsaurar ra’ayi da tashin hankali na addini.

  • Bajintar Aiki: Majalisar Dattawa Ta Jinjina Wa Ministan Yaɗa Labarai
  • Yakin Haraji Da Gwamnatin Amurka Ke Gudanarwa Na Jefa Fargaba a Zukatan Amurkawa

A baya-bayan nan wasu lamura biyu sun wakana a Jihar Oyo wanda ake zargin masu tsattsaurar ra’ayi ne suka haifar da ke tasiri a shiyyar kudu maso yamma, wanda kai tsaye aka fahimci ka iya janyo tashin hankali mai tsauri na addini.

ADVERTISEMENT

Majiyoyi masu tushe sun tabbatar da cewa an sanar da hukumomin tsaro wadannan aikace-aikacen da ake zargin na masu tsautsaurar ra’ayin ne a kudu maso yammacin kasar domin neman daukan matakan gaggawa.

Majiyoyin sun ce tunin aka bayar da umurni ga jami’an tsaro da su bi sawun lamarin a sirrance domin kawo karshen matsalar tun kafin ta yi kamari.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Wata majiya ta ce baya ga barazanar kungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi da ‘yan ta’adda da ke kokarin kutsawa yankin ta tsohon gandun dajin Oyo da dajin Kamoko, wanda ya taso daga jihohin Kaduna da Neja da Kwara da kuma dajin Oyo, akwai rahotannin da ke cewa, wasu kungiyoyi masu tsattsauran ra’ayi suma suna yunkurin shiga yankin Kudu maso Yamma da yada kiyayya ta addini.

An kuma gano cewa jami’an tsaron sun fara binciken wata kungiyar da ke yunkuri kan shari’a wacce a baya-bayan nan ta yi barazanar kafa kotun shari’a a cikin Oyo. Majiyoyin sun ce makonnin da suka gabata jami’an tsaro sun yi tambayoyi ta mutane da dama da suke da alaka da shirin kafa shari’a a Oyo.

Haka kuma an gano cewa yunkurin masu shari’a shi ne don su kafa majalisar shari’a da za ta kula da wasu harkokin jama’a kamar aure, sakin aure da gado, saboda sun fahimci kotunan da ke akwai a halin yanzu sun aminta ne da harkokin kwansitushin.

A halin da ake ciki kuma, jam’iyyar ‘Oodua People’s Congress’ (OPC) karkashin Fredrick Fasheun, ta bukaci daukacin gwamnonin Kudu maso Yamma shida da su dauki matakin gaggawa na tsaro wajen tarwatsa sansanonin ‘yan ta’adda da ke fitowa daga Arewa, a cikin dazuzzukan Yarbawa, tare da yin alkawarin taimaka wa jami’an tsaro wajen magance matsalar barazanar ba tare da bata lokaci ba kafin a makara.

OPC a wata sanarwar da ta fitar, ta ce, a shirye take kuma akwai zaratan da za su taimaka wa jami’an tsaro wajen kawo karshen wadanda ake zargin ‘yan ta’adda ne da suke kwararowa daga arewa zuwa kudu.

Addini
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Next Post
Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Donald Trump

Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Donald Trump

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.