ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Binciki Tashin Rikicin Addini A Kudu Maso Yamma

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Addini

Da yiyuwar gwamnatin tarayya za ta aiwatar da wani bincike na musamman kan wasu harkokin addinai da ke haifar da tashin-tashina na addini a wasu sassan kudu maso yammacin kasar.

A wani binciken da majiyarmu ta gudanar, ya tabbatar mata da cewa gwamnatin tarayya ta nuna damuwarta matuka kan rahotonnin aikace-aikacen da ake samu na wasu kungiyoyin masu tsattsaurar ra’ayi da tashin hankali na addini.

  • Bajintar Aiki: Majalisar Dattawa Ta Jinjina Wa Ministan Yaɗa Labarai
  • Yakin Haraji Da Gwamnatin Amurka Ke Gudanarwa Na Jefa Fargaba a Zukatan Amurkawa

A baya-bayan nan wasu lamura biyu sun wakana a Jihar Oyo wanda ake zargin masu tsattsaurar ra’ayi ne suka haifar da ke tasiri a shiyyar kudu maso yamma, wanda kai tsaye aka fahimci ka iya janyo tashin hankali mai tsauri na addini.

ADVERTISEMENT

Majiyoyi masu tushe sun tabbatar da cewa an sanar da hukumomin tsaro wadannan aikace-aikacen da ake zargin na masu tsautsaurar ra’ayin ne a kudu maso yammacin kasar domin neman daukan matakan gaggawa.

Majiyoyin sun ce tunin aka bayar da umurni ga jami’an tsaro da su bi sawun lamarin a sirrance domin kawo karshen matsalar tun kafin ta yi kamari.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Wata majiya ta ce baya ga barazanar kungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi da ‘yan ta’adda da ke kokarin kutsawa yankin ta tsohon gandun dajin Oyo da dajin Kamoko, wanda ya taso daga jihohin Kaduna da Neja da Kwara da kuma dajin Oyo, akwai rahotannin da ke cewa, wasu kungiyoyi masu tsattsauran ra’ayi suma suna yunkurin shiga yankin Kudu maso Yamma da yada kiyayya ta addini.

An kuma gano cewa jami’an tsaron sun fara binciken wata kungiyar da ke yunkuri kan shari’a wacce a baya-bayan nan ta yi barazanar kafa kotun shari’a a cikin Oyo. Majiyoyin sun ce makonnin da suka gabata jami’an tsaro sun yi tambayoyi ta mutane da dama da suke da alaka da shirin kafa shari’a a Oyo.

Haka kuma an gano cewa yunkurin masu shari’a shi ne don su kafa majalisar shari’a da za ta kula da wasu harkokin jama’a kamar aure, sakin aure da gado, saboda sun fahimci kotunan da ke akwai a halin yanzu sun aminta ne da harkokin kwansitushin.

A halin da ake ciki kuma, jam’iyyar ‘Oodua People’s Congress’ (OPC) karkashin Fredrick Fasheun, ta bukaci daukacin gwamnonin Kudu maso Yamma shida da su dauki matakin gaggawa na tsaro wajen tarwatsa sansanonin ‘yan ta’adda da ke fitowa daga Arewa, a cikin dazuzzukan Yarbawa, tare da yin alkawarin taimaka wa jami’an tsaro wajen magance matsalar barazanar ba tare da bata lokaci ba kafin a makara.

OPC a wata sanarwar da ta fitar, ta ce, a shirye take kuma akwai zaratan da za su taimaka wa jami’an tsaro wajen kawo karshen wadanda ake zargin ‘yan ta’adda ne da suke kwararowa daga arewa zuwa kudu.

Addini
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Donald Trump

Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Donald Trump

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.