• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Buƙatar Amincewar Sanusi Kan Tsare-tsarenmu Na Tattalin Arziki – Minista

by Sulaiman
9 months ago
in Labarai
0
Ministan Labarai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta mayar da martani kan kalaman Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, kan tsare-tsaren gyaran tattalin arziki da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu take aiwatarwa, tana mai bayyana su a matsayin marasa amfani kuma na son rai.

A wata sanarwa da Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya fitar a ranar Laraba, ya bayyana cewa Nijeriya tana cikin wani muhimmin mataki da ke buƙatar matakan da suka dace da kuma ƙarfin hali domin magance manyan matsalolin tattalin arziki.

  • Bukatar Sanin Hakikanin Halin Da Tattalin Arzikin Nijeriya Ke Ciki
  • Jarumin Bollywood Saif Ali Khan Ya Tsallake Rijiya Da Baya

Ministan ya nuna jin daɗin sa kan yadda Sanusi ya amince da wasu tsare-tsaren gwamnati, amma ya nuna damuwa kan yadda Sarkin ya bayyana cewa ba zai goyi bayan gwamnati ba saboda wasu dalilai na son rai.

Ya ce: “Abin takaici ne yadda shugaba daga masarauta mai daraja da son tsare gaskiya da adalci zai fito fili ya ce ba zai faɗi gaskiya ba saboda dalilan kan sa.”

Ya jaddada cewa gyare-gyaren da gwamnatin ta yi, kamar daidaita farashin dala da kuma cire tallafin man fetur, sun zama dole domin magance shekaru na gazawa wajen gudanar da tattalin arzikin ƙasa.

Labarai Masu Nasaba

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Idris ya bayyana cewa an fara ganin sakamakon waɗannan matakai ƙarara, wanda ya haɗa da ƙaruwar ajiyar kuɗaɗen waje, ƙaruwar ƙwarin gwiwar masu zuba hannun jari, da rage yawan bashin da ake biya.

Ministan ya bayyana cewa sukar da sarkin ya yi ba ta dace ba, musamman ganin cewa ya taɓa goyon bayan irin waɗannan matakan a baya. Ya yi kira ga Sanusi da ya fifita cigaban ƙasa a kan son rai.

Ya ce: “Gyaran Nijeriya tana buƙatar haɗin kai, mayar da hankali, da sadaukarwa daga dukkan masu ruwa da tsaki.
“Ya kamata shugabanni su zama jagororin cimma muradun cigaban ƙasa, ba masu tauye amanar jama’a ba.”

Idris ya sake tabbatar da aniyar gwamnatin ta bunƙasa tattalin arziki mai ɗorewa, tare da yin kira ga ’yan Nijeriya su ba da haɗin kai domin samun nasarar waɗannan tsare-tsare.

Ministan ya jaddada cewa gwamnati a shirye take don tattaunawa mai amfani da dukkan masu ruwa da tsaki, tare da tabbatar da cewa tana kan hanyar cika burin samar da ƙasa mai inganci ga kowa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bukatar Sanin Hakikanin Halin Da Tattalin Arzikin Nijeriya Ke Ciki

Next Post

Rikicin Masarautar Kano Ya Sake Daukar Sabon Salo

Related

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

1 hour ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

14 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

15 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

17 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

20 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

22 hours ago
Next Post
Rikicin Masarautar Kano Ya Sake Daukar Sabon Salo

Rikicin Masarautar Kano Ya Sake Daukar Sabon Salo

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.