• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙasashe 7 Sun Mara Wa Nijeriya Baya Don Kafa Cibiyar Koyar Da Ilimin Yaɗa Labarai Ta UNESCO – Minista

by Sulaiman
9 months ago
UNESCO

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa Nijeriya ta samu goyon bayan ƙasashe bakwai tare da alƙawuran ƙasashe 20 domin a kafa Cibiyar Koyar da Ilimin Yaɗa Labarai ta Duniya (IMILI) ta hukumar UNESCO.

 

Ita da UNESCO, ita ce Hukumar Ilimi da Kimiyya da Al’adu ta Majalisar Ɗinkin Duniya.

  • An Kashe Na Biyun Turji A Shugabanci Tare Da Fitattun Kwamandojin ‘Yan Bindiga A Zamfara 
  • Ba Mu Buƙatar Amincewar Sanusi Kan Tsare-tsarenmu Na Tattalin Arziki – Minista

A Turance, IMILI na nufin ‘International Media and Information Literacy Institute’.

 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

Da yake jawabi a Abuja a ranar Talata yayin da ya karɓi baƙuncin tawagar UNESCO da ta zo duba shirin Nijeriya na kafa cibiyar, Idris ya tabbatar da cewa Nijeriya za ta samu amincewar ƙarshe a taron UNESCO na gaba.

 

Ya ce: “Tuni mun samu goyon bayan ƙasashe bakwai, kuma akwai ƙasashe kimanin ashirin da suka nuna shirin su na goyon bayan Nijeriya.

UNESCO

“Mun tabbatar da cewa a taron UNESCO na gaba, za a ba Nijeriya damar kafa MIL a Abuja, a Buɗaɗɗiyar Jami’ar Nijeriya (NOUN).”

 

Ministan ya bayyana farin cikin sa da sakamako mai kyau da aka samu daga tawagar masu duba shirye-shiryen, kuma ya jaddada cewa Nijeriya ta jajirce wajen cika dukkan sharuɗɗan UNESCO na kafa cibiyar.

 

Ya ƙara da cewa wannan shirin ba na Nijeriya kaɗai ba ne, har ma da Afrika da sauran duniya baƙi ɗaya.

 

Ya ce, “Cibiyar Koyar da Ilimin Yaɗa Labarai ba domin al’ummar Nijeriya kawai aka ƙirƙire ta ba, an ƙirƙire ta ne domin al’ummar duniya baki ɗaya.

 

“Wannan wata dama ce ga ƙasar mu ta nuna ƙwarewa, gogewa, da jajircewa kan Ilimin Yaɗa Labarai na duniya.”

 

Idris ya bayyana cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da dukkan kuɗaɗen da ake buƙata domin kafa cibiyar, kuma ya ce Ma’aikatar Yaɗa Labarai tana aiki tare da Ma’aikatar Ilimi da sauran masu ruwa da tsaki domin tabbatar da nasarar shirin.

UNESCO

Ya jaddada cewa Koyar da Ilimin Watsa Labarai yana da matuƙar muhimmanci wajen yaƙi da matsalar yaɗa labaran ƙarya wanda ke barazana ga zaman lafiya da tsaro a duniya.

 

“Yaɗa labaran ƙarya ba matsala ce da ta shafi Nijeriya ita kaɗai ba; matsala ce ta duniya baki ɗaya. Mun yaba da ƙoƙarin da UNESCO ke yi wajen yaƙi da wannan matsalar,” inji Idris.

 

Da yake kira da a haɗa kai a faɗin duniya domin shawo kan wannan matsalar, ministan ya ƙara da cewa yaƙi da baza labaran ƙarya ba yana nufin tauye ’yancin ’yan jarida ne ba.

 

Ya ce: “Domin al’umma ta kasance ’yantacciya kuma dimokiraɗiyya ta bunƙasa, ’yancin ’yan jarida yana da matuƙar muhimmanci. Amma domin samun wannan ’yanci, dole ne mu ɗauki nauyin da ke tare da shi. Ba za ka yi amfani da ’yancin ka wajen tauye haƙƙin wani ba.”

 

A nasa ɓangaren, Mista Nelson Papi Kolliesuah, Babban Manajan Ayyuka na Data-Pop Alliance, wato kamfanin da UNESCO ta ɗauka don tantance shirin da Nijeriya ke yi na kafa cibiyar, ya yaba da ƙoƙarin gwamnatin ƙasar.

 

Ya ce sun zo Nijeriya ne domin tabbatar da cewa an cika sharuɗɗan dukkan kayan aiki, ƙarfin aiki, da tsarin gudanarwa da ake buƙata domin kafa cibiyar.

 

Ya ƙara da cewa sun gamsu da shirye-shiryen da gwamnatin Nijeriya ta yi, inda ya ce cibiyar ta dace da muradun duniya, tsarin ilimi na Nijeriya, da kuma Muradun Cigaba Masu Ɗorewa na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDGs).

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100
Labarai

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi
Labarai

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Next Post
Binciken CGTN Ya Nuna Damuwa Daga Sassan Kasa Da Kasa Game Da Yawaitar Ficewar Amurka Daga Yarjeniyoyin Kasa Da Kasa

Binciken CGTN Ya Nuna Damuwa Daga Sassan Kasa Da Kasa Game Da Yawaitar Ficewar Amurka Daga Yarjeniyoyin Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
UNESCO

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.