• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Za Su Maka Gwamnati A Kotu Kan Karin Kudin Kiran Waya

by Khalid Idris Doya
7 months ago
in Labarai
0
‘Yan Nijeriya Za Su Maka Gwamnati A Kotu Kan Karin Kudin Kiran Waya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan Nijeriya sun sha alwashn maka gwamnatin tarayya a kotu bisa amincewa da ta yi da karin kudin kiran waya da data da sauran caji-cajin da kamfanonin sadarwa ke yi.

Kwatsam sakamakon wannan lamarin, masu hada-hadar kudade ta PoS sun kara kudin cazan jama’a da suke yi.

  • Shirin Tallafinmu Ga Nijeriya A 2025 Zai Kai Ga Asalin Mabukata – Wakilin MDD
  • Jagoranci Nagari: Kungiyar Lauyoyi Ta Karrama Gwamnan Zamfara Da Lambar Yabo

Shugaban kungiyar masu amfani da layukan sadarwa, Adeolu Ogunbanjo da kuma jami’in watsa labarai na kungiyar masu mu’amala da kudade ta wayar tarho da wakilansu na bankuna a Nijeriya, Ogungbayi Ganiyu su ne suka tabbatar da shirin garzawa kotu a hirarsu da ‘yan jarida a ranar Litinin.

Wannan na zuwa ne dai bayan sahalewar da hukumar kula da sadarwa ta Nijeriya (NCC) ta bayar ga kamfanonin sadarwa da su kara kudaden cajin da suke yi da kaso 50 a cikin 100.

Ministan sadarwa da tattalin arziki na zamani, Bosun Tijani, shi ne ya amince wa kamfanonin da su yi karin biyo bayan zaman da suka yi da shi da suka nemi yin karin kaso 100 na cajin da suke yi ga al’ummar Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Wannnan karin kuma na zuwa ne bayan shekaru 13 tun bayan da NCC ta sanar da farashin jaddawalin cajin da kamfanonin za su yi a shekarar 2013.

LEADERSHIP HAUSA ta labarto cewa da wannan sabon karin na nuni da cewa kamfanonin za su cazan ‘yan Nijeriya naira 16.5 a kowace kiran waya na minti daya daga naira 11, yayin da tura sakon kar-ta-kwana ya koma naira 6 daga naira 4, sannan data na gigabit kwara daya zai koma naira 431.25.

Da yake suka kan matakin, Ogunbanjo ya nemi masu amfani da layukan sadarwa da su yi tir da kin amincewa da karin, inda yake cewa masu amfani da layukan sun amince a yi karin kaso 5 ko 19 kacal ba wai kaso 50 da NCC ta sanar ba.

Ya lura kan cewa masu amfani da layukan sadarwar sun amince da su gurfanar da gwamnatin tarayya a kotu bisa amincewa da ta yi da karin kaso 50 na caje-cajen kamfanonin sadarwa.

Ogunbanjo ya koka kan cewa karin zai kara jefa jama’a cikin matsin rayuwa da suke fama da shi sakamakon janye tallafin mai wanda ya janyo tashin farashin sufuri da kayan abinci, wanda ya kai kaso 38.90 a watan Disamban 2024.

“Abun takaici ne sanarwar da karin farashin kiran waya da na data da minista ya yi, kuma za mu je kotu mu kalubalanci wannan amincewar karin kaso 50 da gwamnatin tarayya ya yi domin mu mun amince da karin kaso 5 ko 10 kacal ne. Su kamfanonin sadarwar kudi kawai suke son yi a kan masu amfani da layukansu,” ya koka.

Shi kuma jami’in yada labarai na kungiyar masu mu’amala da kudade ta wayar tarho da wakilansu na bankuna a Nijeriya, Ogungbayi Ganiyu, ya ce, mambobinsu ba su da wani zabi illa su kara kudin cajin da suke yi wa jama’a.

Ya ce, mambobin suna tsakamai wuya, musamman ta fuskanci sayar da data, kuma tilas jama’a su ga sauyi bisa wannan karin da NCC ta amince da shi.

Daga nan ya ce jami’an da ke sarrafa PoS da yiwuwar su kara kudin cajin da suke yi domin hakan ne ya zama musu dole.

Karin kudin kira da na data da sauran cajin kamfanonin sadarwar ana tunanin zai fara aiki ne daga watan Fabrairun 2025, ya zama wani karin tsarin manufar gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da ke kara janyo matsin rayuwa ga al’umma.

A kwanakin baya ne dai kamfanonin sadarwar suka yi barazanar cewa muddin ba a amince musu da karin kudin da suka tatsar jama’a ba, to tabbas za su rufe ayyukansu a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KaraKiran WayaKotu
ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

Related

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho
Labarai

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

35 minutes ago
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata
Labarai

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

2 hours ago
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja
Manyan Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

3 hours ago
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto
Labarai

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

16 hours ago
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

21 hours ago
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

22 hours ago
Next Post
Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

LABARAI MASU NASABA

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

August 10, 2025
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

August 10, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

August 10, 2025
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

August 10, 2025
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.