ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jagoranci Nagari: Kungiyar Lauyoyi Ta Karrama Gwamnan Zamfara Da Lambar Yabo

by Sulaiman
1 year ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada cewa tabbatar da doka da oda na buƙatar ƙwarewa ta fasaha, jajircewa da kuma gaskiya da riƙon amana.

 

Gwamna Lawal ya kasance babban baƙo a wajen taron shari’a na shekara-shekara ta 2024 da Ƙungiyar Lauyoyi ta Ƙasa (NBA) reshen Gusau ta shirya.

ADVERTISEMENT
  • Saudiyya Ta Ware Dala Biliyan 100 Don Sabunta Masallatan Harami
  • Sin Da AU Sun Cimma Nasarori A Fannonin Diflomasiyya Da Tattalin Arziki

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa a yayin taron, gwamna Lawal ya samu lambar yabo ta karramawa a matsayin babban abin tunawa kuma mutum mai tasiri ga al’ummar jihar Zamfara.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Ya ƙara da cewa, shugaban NBA reshen Gusau Mu’azu Shehu Ahmad Esq ne ya ba gwamnan lambar yabon.

 

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya sake nanata cewa taro kamar na NBA yana ƙara ƙwarin gwiwa ga ƙwararrun lauya don musayar ra’ayoyi da inganta samar da adalci, dimokuraɗiyya, da bin doka.

 

Ya ce, “Taken taron na bana shi ne; “Tabbatar da Doka: Ginshiƙin Ci gaban Dimokraɗiyya”. Yana nuna da irin rawar da fannin shari’a ke takawa wajen tsara al’ummarmu ta hanyar tabbatar da kyawawan ɗabi’u, adalci da riƙon amana.

 

“Ina da yaƙinin cewa za mu iya ƙarfafa ginshiƙin dimokuraɗiyyar mu da kuma ginshiƙin wanzuwar mu a matsayin al’umma ta hanyar sadaukar da kai ga bin doka da oda.

 

“A halin da ake ciki, ina yaba wa Ƙungiyar Lauyoyin Nijeriya reshen Gusau, bisa namijin ƙoƙarin da suke yi na tabbatar da adalci da bin doka da oda. Haƙiƙa sadaukarwar da kuka yi ga wannan aiki mai daraja abin a yaba ne kuma abin koyi ne.

 

“Ina kira gare ku da ku ci gaba da nuan halin ƙwarai na ma’aikatan shari’a don tabbatar da cewa kun kasance ginshiƙin fata ga talakawa da duk masu neman adalci.

 

“Na yaba wa ƙoƙarin lauyoyi wajen ganin an yi adalci ba tare da nuna son kai ba cikin gaggawa, har a lokutan da ake fuskantar ƙalubale. Tsayuwarku ta kasance ƙwarin gwiwa kuma ta zama abin tunatarwa cewa adalci shi ne ginshiƙin kowace al’umma mai wayewa.

 

“Gwamnatin jihar Zamfara ta tsaya tsayin daka wajen dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali. Muna aiki tuƙuru don magance matsalolin rashin tsaro da samar da yanayin da al’ummarmu za su zauna ba tare da tsoro ba.

 

“Ina kuma so in jaddada muhimmancin ilimin shari’a wajen ƙarfafa tsarin adalcinmu.

 

“Tsarin ilimin shari’a yana buƙatar karatu da haƙiƙa. Ina roƙon ku da ku riƙa amfanar juna wajen da horo da ilimin da ku ka samu, kamar wannan taro na makon shari’a, don kasancewa a sahun gaba wajen aiki da doka.

 

“A wannan lokaci, ina miƙa godiya ta ga waɗanda suka shirya wannan babbar lambar yabo a gare ni. Jajircewar da na yi na yaƙar rashin tsaro, da bin doka da oda, da gina ababen more rayuwa abin a yaba ne matuƙa.

 

“Ba abin alfahari ba ne kawai, a’a, shaida ce ga namijin ƙoƙarin da duk waɗanda suka yi aiki tare da ni suka yi wajen gina jihar Zamfara mai tsaro, da adalci, da wadata cikin watanni 20 da suka gabata.

 

“A ƙarshe, yayin da nake yaba wa Ƙungiyar Lauyoyi ta Nijeriya reshen Gusau, kan yadda suka saba shirya wannan taron na shekara-shekara, cikin alfahari nake bayyana buɗe makon taron shari’a na 2024. Ina addu’ar shawarwarinku su kasance masu ma’ana da tasiri. Allah Ta’ala Ya yi mana jagora a cikin ayyukanmu baki ɗaya”.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Sabon Albishir Ga Masu Kawo Ziyara Ko Yada Zango A Birnin Beijing Na Kasar Sin

Sabon Albishir Ga Masu Kawo Ziyara Ko Yada Zango A Birnin Beijing Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.