• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (4)

by Idris Aliyu Daudawa
9 months ago
Ilimi

Bugu da kari jami’an ilimi suna iya suna lura da yadda za a tafiyar da kasafin kudin makaranta ko hukumar da ke da alaka da ilimi,samar da hanyoyin da suka dace  da lamarin tallace- tallace,yadda za ‘a dauki Malamai, da ci gaba da tafiyar da lamura da su.

Idan ana bukatar samun nasara ta wannan bangare a matsayin sun a jami’an ilimi dole su kasance sun mallaki dabarun da za su taimaka ma su yin mu’amala, yin hulda,kai har ma da ganewa da fahimtar manufofin ilimi da yadda ake tafiyar da su.

  • Kasar Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Na Gwaji A Kan Fasahar Sadarwa
  • Sinawa Kimanin Miliyan 1.85 Za Su Rika Zuwa Yawon Bude Ido a Ketare Kullum Lokacin Hutun Bikin Bazara

Su san yadda za su lamarin da ya shafi aikinsu da masu fada aji/ruwa da tsaki,da suka hada da Iyaye, ‘yan makaranta/ dalibai, Malamai,da sauran kwararru.

Akwai kuma bukatar su rika yin tunani mai inganci,da kuma kirkirar abu, su kuma kasance suna tafiya daidai da zamani da yadda lamarin ilimin yake.

Gaba daya kacokam shi/su jami’in/ jami’an ilimi ayyukansu suna matukar wahala,sai dai akwai daukaka,lamarin da yake bukatar wanda/ wadanda suka amsa sunan sun mallaki yin tunani mai amfanarwa da wasu dabaru na nuna kauna ga lamarin daya shafi ilimi.

LABARAI MASU NASABA

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ko suna aiki a makarantar Firamare ne ko, jami’a, jami’an ilimi suna bada muhimmiyar gudunmawa ta shata yadda al’umma  za su iya kasancewa a gaba,da kuma tabbatar da cewa suna samun ilimi mai nagarta da taimaka masu domin cimma burinsu.

Dabarun Da Suka Kamata Jami’an Ilimi Su Mallaka

Sanin kowa ne jami’in ilimi kan shi ne alhakin tafiyar da al’amuran tsare- tsare da manufofin ilimi suka rataya kan shi, na makarantu da hukumomi.

Su ne wadanda ke a sahun gaba wajen lamarin da ya shafi ci gaban ilimi.

Ayyukan su suna da yawa shi yasa akwai bukatar su kasance sun mallaki/ko suna da dabarun da za su taimaka masu tafiyar da ayyukan su kamar yadda suka kamata.

Manyan dabarun da ake bukatar jami’in ilimi yana da su sun hada da babban lamari na yin mu’amala ta kud da kud da mutane, dabarar bincike da kuma nazari, yadda za a tafiyar da ayyuka,maganin matsalolin da za su iya tasowa, fahimta sosai tsare- tsare, da dokokin ilimi.

Yadda za ayi tuntuba ta sadarwa da masu ruwa da tsaki wadanda suke da yawa, da suka hada da Malamai, Iyaye, da kuma jami’an makarantu.

Ba ma kamar yadda za su tafiyar da manufofi da tsare- tsaren ilimi masu rikitarwa, su fahimci abubuwan da duk lamurran suka kunsa.

Jami’in ilimi akwai bukatar ace koda wane lokaci ya san halin da ake ciki na lamuran da suka shafi ilimi.Tafiyar da ayyukan ilimi wannan ma ana bukatar hakan ga jami’in ilimi  ace ya san su,tsare-tsare da yadda za a aiwatar da su.

Hakanan ma akwai bukatar su tsara,shirya sosai,wajen aiwatar da yin ayyuka da tabbatar da kammala su cikin lokaci da kuma kudin da aka ware masu.

Dabarar da za ayi maganin matsaloli wannan ma ana sa ran jami’in ilimi ya mallaki hakan,su gano inda matsalolin suke da yadda za su yi maganin su manufofi da tsare- tsaren ilimi har ma da aiwatar da su,ana bukatar jami’in ilimi ya san da hakan.

Ana ma bukatar su ya zama sun sani sosai tsare- tsaren, dokokin  ilimi karamar hukuma, Jiha, da kuma gwamnatin tarayya, wajen tabbatar da ana aiwatar da su kamar yadda dokoki suka tanadar kamar yadda ya dace.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

gombe
Ilimi

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma
Ilimi

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
ASUU
Ilimi

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Next Post
Fursunoni 48,932 Ke Jiran Shari’a A Gidajen Yarin Nijeriya – Mukaddaashin Kwantirola

Fursunoni 48,932 Ke Jiran Shari'a A Gidajen Yarin Nijeriya - Mukaddaashin Kwantirola

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Ɗan Fashi Sanye Da Kayan NYSC A Enugu

October 21, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.