• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Laifi Don Musulmi Sun Yi Murnar Shigar Sabuwar Shekarar Musulunci

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
3 years ago
in Dausayin Musulunci
0
Ba Laifi Don Musulmi Sun Yi Murnar Shigar Sabuwar Shekarar Musulunci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ba laifi idan an yi murna ta shigar sabuwar shekarar Musulunci.

Ba za a bi na wadanda za su bidi’antar da abin ba, domin hatta murnar haihuwar Manzon Allah (SAW) sun ce bidi’a ne.

  • Tinubu Ga Peter Obi: Ka Gargaɗi Magoya Bayanka Kan Ɓata Min Suna
  • Kasar Sin Ta Bukaci A Tallafa Wa Kasashen Afirka Don Inganta Karfinsu

Har kai kanka ma za su iya ce maka bidi’a, saboda ba ka zo a zamaninsa ba.

Masu wannan fahimtar Malamai sun ce ba wai suna nufin a koma wa Sunnar Manzon Allah ba ne, suna so ne a koma wa zamanin Annabi (SAW), ka ge ke nan sai mu ajiye su motoci da sauran kayan kere-kere na fasaha da ake amfani da su yanzu har da su lantarki da su jirgin sama duk a ajiye, a koma amfani da su rakuma da dawaki da jakuna.

Idan kayan yaki ne ma a ajiye su nukiliya, da manyan tankokin yaki da su jiragen yaki sai dai a yi amfani da su kwari da baka da takubba, idan an tari abokan gaba da wadannan an yi bidi’a kamar yadda fahimtar wadancan mutanen take. Ka ga idan aka yi haka ai hankali ya warware.

Labarai Masu Nasaba

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)

Kur’anin da Allah ya saukar mana zamaninsa ba ya shudewa, ya dace da kowane irin zamani da ya zo, ko zai zo a nan gaba.

Ayoyin da suka sauka suna nan suna mana hukunci, ba a kula da ko dan waye suka sauka, ko don me suka sauka, abin ya zama hukunci ga al’ummar Annabi duka tun daga wancan zamanin da aka saukar har zuwa tashin kiyama.

Misali ayar da ta ce, “ku sani, hakika Annabi yana cikinku”, wasu sai su ce da su Sayyidina Abubakar ake, ban da mu a zamanin nan. Alhali kuwa ba haka ba ne, duka Malamai na Allah sun fassara wannan da cewa Annabi (SAW) yana nan a cikin al’ummarsa har zuwa tashin kiyama.

Idan kuwa masu wancan fahimtar suka dage sam sai an tsame Annabi ba ya tare da da al’ummarsa, sai mu ce, ke nan ayar da ta umurce mu mu kadaita Allah “ku yi sani babu abin bautawa da gaskiya sai Allah” da Sahabbai kawai ake yi.

Kun ga ai babu wanda zai karbi wannan. To, haka shari’ar Manzon Allah take, ta dace da duk irin sauyin da za a samu na zamani.

Akwai hadisai da yawa da Annabi (SAW) yake so ya ga al’ummarsa tana cikin nishadi ba cikin kunci ba. Manzon Allah yana so ya ga Musulmi ya fita daban da saura kamar kitse a cikin nama, ya yi ado ya yi kyau.

Don haka, za mu yi murnar shiga sabuwar shekarar Musulunci, ba bidi’a ba ne, sunnah ce ta Manzon Allah, sunnah ce ta Khalifofinsa, Musulmi su yi murna su yi nishadi. Addini ba ya zo ne ya tattakure mutane ya hana su sakat ba, har ma a samu wasu suna barin addini zuwa wasu saboda takura, a uzu billahi.

Irin haka ta faru a Ibadan, wasu Musulmi sun kawo kara wurin Shehu Ibrahim cewa matasansu suna zuwa coci saboda kidar da ake yi a can, Shehu ya ce musu to ku wa ya hana ku kidar? Ka ga dole (masu irin waccan fahimtar) su shiga karatu sosai a nan wurin (kafin su kai ga cewa kaza ya haramta, kaza ya halasta).

Saboda haka a bar mutane su yi murnar shiga sabuwar shekarar Musulunci, Sarkin Musulmi ya sanar, Malamai su yi bayani, al’ummar musulmi su taya juna murna, Alhamdu lillah.

Kamar yadda muka fada, yana daga cikin abin da ya sa Sahabbai ba su sanya farkon shekarar Musulunci a Rabi’ul Auwal ba don kar a hade manyan bukukuwanmu biyu a wuri daya, ga bikin haihuwar Annabi (SAW) ga kuma na shiga sabuwar shekara, kamar dai yadda Sayyidina Aliyu (Karramallahu wajhahu) ya hana a yi ramakon Ramadan a cikin goman farko na watan Zulhajji, don kar wani ya kwace wani, alhali kowannensu yana da girmansa da falalarsa.

Don haka, a bar Mauludin Manzon Allah da girmansa da falalarsa, shi ma shiga sabuwar shekarar Musulunci a barshi da nashi.

Sannan me ya sa Sahabbai ba su kafa shekarar ta Musulunci da ranar da aka aiko Manzon Allah da Manzanci ba, sai dai Hijira?.

Haka nan me ya sa ba su kafa da ranar da aka kammala saukar da Shari’ar Manzon Allah (SAW) ba, ko ranar Fatahu Makkata (ranar da aka bude Makka)? Sahabbai duk sun san da girma da falalar wadannan ranakun, amma duk idan aka hadasu, daya zai kwace wa daya.

Alheran da ke cikin falalar Hijira suna da yawa. Daga ciki shi ne ‘yan’uwatanka da Manzon Allah ya hada a tsakanin Muhajirai da Ansaru, mutanen Makka da masu masaukinsu na Madina. Haka nan da ‘yan’uwantaka a tsakanin su kansu Muhajiran, kamar yadda ya hada a tsakanin Sayyidina Hamza (RA), wanda yake Baffansa, Balarabe, Bakuraishe da kuma bawansa mai masa hidima Zaidu bin Harisata.

Kuma saboda wannan ‘yan’uwantakar, Zaidu ya shiga cikin su Sayyidina Aliyu da wansa Ja’afaru bin Abiy dalibi wajen neman a bashi rainon ‘yar Sayyidina Hamza wadda Manzon Allah ya taho da ita daga Makka lokacin da ya je ramuwar Umura.

Da aka tambaye shi me ya sa yake so a bashi rainonta, Zaidu ya ce saboda ‘yar dan’uwana ce. To daga baya dai Manzon Allah ya bai wa Ja’afar ita saboda bayan kasancewarta ‘yar Baffansa yana kuma aure da ‘yar’uwar mahaifiyarta.

To, ka ga girman ‘yan’uwantaka ta Musulunci. Irin wannan ma ana gani kuru-kuru a tsakanin wadanda suka sha Faila, ‘yan’uwa su shaku da juna su zama uwa daya uba daya.

Haka shauran Musulmi ma duk a yi kokari a zama haka. ‘Yan’uwantaka in ta faru, komai ya faru, idan soyayya ta samu komai ya samu.

Kafin Hijira, Manzon Allah (SAW) ya koya mana yadda za mu yi addini idan ka tsinci kanka a cikin wadanda ba musulmi ba kuma ba su yarda da Musulunci ba, kamar yadda ya rika yin sallah a Ka’aba duk kuwa da kasancewar daruruwan gumaka a ciki.

Yana sallah yana kallon Ka’aba kuma da gumaka a ciki sannan bai ce zai cire ko daya ba, shi dai ya san Allah yake wa sallah ba gumaka ba.

Haka nan ya koyar da yadda za a yi addini a wurin mutanen da za su barka ka yi addininka, amma ba su so ka kawo musu naka ka bata musu tsarinsu, kamar yadda Sahabbai suka yi a Habasha. Saboda kyawawan halayensu da wasu ‘yan garin suka gani suka musulunta bisa radin kansu.

Don haka kar mutum ya yi ta fada ya ce dole sai ya sauya wa mutanen da yake cikinsu tsarinsu da suka yarda da shi.

Manzon Allah ya nuna mana zama a kasar da Musulmi sun fi yawa amma kuma akwai wadanda ba musulmi ba a ciki, kamar zaman Madina.

Ya kulla yarjejeniyar zaman lafiya da wadanda ba musulmin ba. A kare wa duk ‘yan kasa hakki bisa tsarin zamantakewarsu, duk abin da zai amfani kasa na kowa ne, haka nan duk abin da zai cuci kasa ya shafi kowa za a fito a yi taron dangi a kai.

Haka aka zauna har sai da Yahudawa suka ha’inci Manzon Allah (SAW) ya kore wasu daga Madina wasu kuma aka kashesu.

Kuma duk da wannan, Manzon Allah (SAW) saboda shi Annabin Rahama ne ya ba Yahudawan dama su zabi alkalin da zai musu hukuncin abin da suka yi, suka zabi Sa’adu bin Mu’azu. Hukuncin da ya yanke kuma Manzon Allah (SAW) ya ce ya yi dai-dai da hukuncin da Allah ya yanke.

Don haka, ko da wani zai ce ai Manzon Allah ya yanka Yahudawan Banu kuraiza don ya samu kafar ta da rikici a kasa, sai a ce masa ba haka abin yake ba. Su Banu kuraiza hukuncin da ya dace da su kenan a ka’idar duniya.

Duk wanda ya ha’inci kasarsa ya hada kai da abokan gaba ana yaki hukuncin kisa ya hau kansa. Kuma ko waye ba Musulmi ba kawai irin hukuncin da zai yi kenan.

Haka aka kori Banud Nadir da Banu kainu ka’a, Madina ta zama kasar Musulunci, Manzon Allah (SAW) shi ne shugaba mai shari’a da littafin Allah Alkur’ani. Duk dai abin da za mu koya mu yi aiki da shi ne zaman Manzon Allah a Makka, zaman Sahabbansa a Habasha da kuma zamansa a Madina (SAW).

Wannan yana daga cikin albarkar Hijira.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Annabi SAWMurnar Sabuwae Shekarar MusulunciSahabbaiSallahTambaya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsadar Farashi: Yadda ‘Yan Nijeriya Suka Koma Sayen Kaya Masu Araha

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa
Dausayin Musulunci

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

1 week ago
Ramadan
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)

2 weeks ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni

3 weeks ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci

4 weeks ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (1)
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (1)

1 month ago
Yadda Azumi Yake Sa Tsoron Allah
Dausayin Musulunci

Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu

2 months ago
Next Post
Goron Juma’a

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

May 11, 2025
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

May 10, 2025
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

May 10, 2025
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.