• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalaman Trump Marasa Kan-gado Game Da Gaza Za Su Kara Tsananta Halin Da Ake Ciki A Gabas Ta tsakiya

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
Trump

Kalaman da shugaban kasar Amurka Donald Trump ya yi kan batun zirin Gaza a kwanan baya, ta sake girgiza al’ummar duniya.

A zantawarsa da kafar yada labarai ta FOX News, Donald Trump ya bayyana cewa, za a kori Falasdinawa daga zirin Gaza har abada, kuma ba su da ikon sake komawa. A wani sa’in kuma ya ce, “Ni zan mallake shi, wuri mai kyau da zan yi cinikin gidaje, ba zan kashe kudi da yawa ba game da hakan.”

  • Malaman Makaranta Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi Sun Tsunduma Yajin Aiki A Abuja
  • Maryam Malika Ta Buƙaci Kotu Ta Tabbatar Da Sakin Da Mijinta Yayi Mata

Trump ya hade burinsa na siyasa tare da basirarsa ta kasuwanci da cinikin gidaje wuri guda, yana son cimma burinsa ta hanyar keta hakkin Palasdinawa, kuma mambar mahukuntan kungiyar Hamas, Izzat al-Risheq ya bayyana kalaman shugaban a matsayin abin ban dariya da rashin imani da toshewar basira. Ya jadadda cewa, “Trump ya daidaita batun Gaza da halayyarsa ta dan kasuwa mai cinikin gidaje kuma ba zai cimma nasara ba ko kadan. Mu Falasdinawa ba za mu yarda da ko wane mataki na sa mu yin kaura ko kore mu daga yankin ba ko kadan.”

Zirin Gaza na matukar bukatar tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali na dogon lokaci ta shirin “samar da kasashe biyu”, kuma Falasdinawa ba za su samu farfadowa ba har sai an tabbatar da bukatun nan. Ikirarin da Amurka ke yi na karbe ikon mallakar zirin ba shi da asali a karkashin shari’a da doka, mataki ne kawai da zai keta dokar duniya, har ma da tsananta halin da ake ciki a gabas ta tsakiya, kuma zai sake jefa yankin cikin munanan tashe-tashen hankula marasa tabbas.

Donald Trump shugaban kasar Amurka ne kawai, don haka, ba ruwansa da yin katsalandan cikin harkokin gabas ta tsakiya da na sauran kasashen duniya. (Mai zane da rubutu: MINA)

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika
Daga Birnin Sin

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
Next Post
Jakadan Sin Ga Amurka: Haraji Da Yakin Kasuwanci Ba Za Su Iya Kawo Cikas Ga Ci Gaban Sin Ba

Jakadan Sin Ga Amurka: Haraji Da Yakin Kasuwanci Ba Za Su Iya Kawo Cikas Ga Ci Gaban Sin Ba

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.