ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojojin Nijeriya Za Su Fara Karɓar N3,000 Kudin Abinci A Rana

by Abubakar Sulaiman
9 months ago
Nijeriya

Babban hafsan Sojojin Nijeriya (COAS), Laftanar Janar Olufemi Oluyede, ya nuna damuwa kan ƙarancin kuɗin abinci da ake bai wa Sojoji a kullum, wanda a halin yanzu ke kan N1,500.

Yayin da yake jawabi ga jami’ai da sojojin Rundunar 81 ta Sojojin Nijeriya a filin taro na 9th Brigade da ke Lagos, Janar Oluyede ya sanar da cewa nan da ƙarshen wata mai zuwa, za a ƙara wannan kuɗi zuwa N3,000 a rana.

Baya ga wannan ƙari, Janar Oluyede ya bayyana cewa Rundunar Sojojin Nijeriya ta ƙaddamar da shirin lamuni mai ragi na 3% domin tallafa wa Sojoji wajen aiwatar da ayyukan ci gaban kansu. Duk da haka, ya ja hankalin Sojojin da su nemi bashin ne kawai idan lallai suna buƙata, domin yana iya zama ƙalubale wajen biyan sa, ko da yake kuɗin ruwan kan bashin kaɗan a cewarsa.

ADVERTISEMENT
  • Gwamna Buni Ya Jaddada Bai Wa Sojoji Gudunmawar Kawo Karshen Boko Haram 
  • Kakakin Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ya Yi Fatali Da Zargin Australia A Kan Atisayen Sojojin Kasar

Dangane da matsalar gidaje, babban hafsan Sojojin ya amince cewa da yawan Warrant Officers suna fuskantar matsalar rashin mallakar gidajensu bayan ritaya. A sakamakon haka, ya ce rundunar ta faɗaɗa shirin samar da gidaje masu sauƙin kudi ga Sojoji a wurare daban-daban da suka haɗa da Abuja, Ibadan, Jos, Fatakwal, Owerri da Akwa Ibom.

Wannan mataki na ƙarin kuɗin abinci da tallafin bashi da kuma shirin gidaje yana daga cikin sauye-sauyen da rundunar ke yi domin inganta rayuwar Sojojin da ke aiki, tare da basu ƙwarin gwuiwa wajen gudanar da aiyukansu.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon
Manyan Labarai

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

November 17, 2025
Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja
Manyan Labarai

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
Manyan Labarai

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Za Ta Duba Ƙarin Farashin Wutar Lantarki

Gwamnatin Tarayya Za Ta Duba Ƙarin Farashin Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

November 17, 2025
Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.