• English
  • Business News
Wednesday, May 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

BUK Ta Kori Ɗalibai 62, Ta Dakatar da 17 Saboda Satar Jarrabawa

by Naziru Adam Ibrahim
3 months ago
in Labarai
0
BUK Ta Kori Ɗalibai 62, Ta Dakatar da 17 Saboda Satar Jarrabawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’ar Bayero ta Kano (BUK), ta aiwatar da tsattsauran mataki kan ɗaliban da aka samu da laifin satar jarrabawa, inda ta kori 62, tare da dakatar da 17 kamar yadda Ƙa’idojin dokokin jarrabawa da karatu na jami’a (GEAR), suka tanada.

An yanke wannan hukunci ne yayin zaman majalisar dattijan jami’ar karo na 421, da ya gudana a ranar 26 ga watan Fabrairu 2025, bayan tabbatar da ɗaliban sun aikata laifuka daban-daban na satar jarrabawa da sauran ayyukan rashin gaskiya.

  • Jami’ar Bayero Ta Shirya Bikin Yaye Ɗalibai Karo Na 39
  • Kotu Ta Dakatar Da Yunkurin Aminu Ado Bayero Na Gyaran Fadar Nassarawa

Cikin rahoton sanar da korar wanda ke ƙunshe a jaridar mako-mako ta jami’ar, ta bayyana cewa matakin na daga ƙoƙarin BUK na kare darajar ilimi da tabbatar da bin ƙa’idojin jarrabawarta.

Baya ga korar, jami’ar ta dakatar da wasu ɗalibai 17 na wani taƙaitaccen lokaci a matsayin ladabtarwa, inda aka wanke wasu ɗalibai 5 bayan bincike ya tabbatar da ba su da laifinsu.

Kazalika an gargadi ɗalibai 29 kan munin aikata laifin satar jarrabawa, wanda ke nuna matsayar BUK na rashin sassauci kan irin waɗannan laifuka, kana an ɗage yanke hukunci kan wasu ɗalibai uku domin ci gaba da nazari da kuma tattara ƙarin hujjoji kafin a hukuncin ƙarshe.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice

Mutum 1 Ya Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Mummunan Hatsarin Mota A Abuja

Daga ƙarshe sanarwar ta ƙara jaddada ingantattun ƙa’idojin karatu a BUK, wanda ta ce ba za ta lamunci satar jarrabawa ko laifuffuka makamantan haka ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Aikin Noma Ya Ragu Da Kashi 1.8 A Zango Na Hudu A Shekarar 2024

Next Post

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

Related

Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice
Tsaro

Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice

1 hour ago
Mutum 1 Ya Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Mummunan Hatsarin Mota A Abuja
Labarai

Mutum 1 Ya Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Mummunan Hatsarin Mota A Abuja

3 hours ago
Gwamna Uba Sani Ya Kammala Titin Unguwar Su El-Rufai
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Kammala Titin Unguwar Su El-Rufai

4 hours ago
Sojoji Sun Koka Bisa Jinkirin Yanke wa Ƴan Ta’adda 1,450 Hukunci
Tsaro

Sojoji Sun Koka Bisa Jinkirin Yanke wa Ƴan Ta’adda 1,450 Hukunci

6 hours ago
Kotu Ta Ci Tarar  El-Rufai Miliyan 900 Saboda Wani Laifi Da Ya Yi A 2019
Manyan Labarai

Kotu Ta Ci Tarar  El-Rufai Miliyan 900 Saboda Wani Laifi Da Ya Yi A 2019

7 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wani Ɗan Bindiga, Sun Ƙwato Makamai Bayan Artabu A Taraba

17 hours ago
Next Post
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

LABARAI MASU NASABA

Taron Kolin ASEAN: Sin Da GCC Na Da Matukar Muhimmanci

Taron Kolin ASEAN: Sin Da GCC Na Da Matukar Muhimmanci

May 28, 2025
Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice

Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice

May 28, 2025
Mutum 1 Ya Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Mummunan Hatsarin Mota A Abuja

Mutum 1 Ya Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Mummunan Hatsarin Mota A Abuja

May 28, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Kammala Titin Unguwar Su El-Rufai

Gwamna Uba Sani Ya Kammala Titin Unguwar Su El-Rufai

May 28, 2025
Unity Cup: Yau Nijeriya Da Ghana Zasu Kece Raini A Birnin Landan

Unity Cup: Yau Nijeriya Da Ghana Zasu Kece Raini A Birnin Landan

May 28, 2025
Sojoji Sun Koka Bisa Jinkirin Yanke wa Ƴan Ta’adda 1,450 Hukunci

Sojoji Sun Koka Bisa Jinkirin Yanke wa Ƴan Ta’adda 1,450 Hukunci

May 28, 2025
Kotu Ta Ci Tarar  El-Rufai Miliyan 900 Saboda Wani Laifi Da Ya Yi A 2019

Kotu Ta Ci Tarar  El-Rufai Miliyan 900 Saboda Wani Laifi Da Ya Yi A 2019

May 28, 2025
An Gudanar Da Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC Karo Na Farko

An Gudanar Da Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC Karo Na Farko

May 27, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wani Ɗan Bindiga, Sun Ƙwato Makamai Bayan Artabu A Taraba

May 27, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashen Afirka

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashen Afirka

May 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.