Shugabannin manyan kamfanonin duniya da wakilan kungiyoyin ‘yan kasuwa, sun bayyana kasar Sin a matsayin “cibiyar zuba jari da raya masana’antu” tare da bayyana aniyarsu ta fadada zuba jari da hadin gwiwa da kasar Sin.
Manyan ‘yan kasuwar sun bayyana haka ne a jiya Juma’a yayin ganawarsu da shugaban kasar Sin Xi Jinping. Ganawar da ta samu halartar shugabannin manyan kamfanonin duniya da wakilan kungiyoyin ‘yan kasuwa fiye da 40.
- Shugaba Xi Ya Jajantawa Shugaban Myanmar Game Da Girgizar Kasar Da Ta Auku
- Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)
A ganin masu zuba jari, yanayin tabbas shi suke bukata don neman habaka kamfanoninsu. Kana yanayin tabbas da ake samu a kasar Sin, ya samo asali ne daga manufofin kasar. Kamar yadda shugaba Xi Jinping ya jaddada a yayin ganawar, “kasar Sin za ta kara bude kofa ga duniya, kuma manufarta ta yin amfani da jarin waje ba ta canja ba, kuma ba za ta canja ba a nan gaba.”
Ban da haka, yanayin tabbas na Sin ya zo ne daga yanayin ci gaba mai aminci da tsaro. Kasar Sin har kullum tana kokarin kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali ta fuskar siyasa, kuma an amince da ita a matsayin daya daga cikin kasashe mafiya aminci da tsaro a duniya. Saboda haka ana iya zuba jari da yin ciniki a kasar Sin ba tare da damuwa ba.
Bugu da kari, shekarar 2025 za ta zama wani muhimmin lokaci na raya kimiyya da fasaha a kasar Sin. Ana iya sa ran ganin kamfanonin kasashen waje sun samu karin damammakin raya harkoki tare da tabbatar da moriyarsu a kasar Sin. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp