ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
Sin

A matsayin babban taron tattalin arziki na farko bayan taron cikakken zama na 4 na kwamitin tsakiya na 20 na jam’iyyar JKS, shugabannin kamfanoni masu yawa a bikin CIIE sun yaba wa damar ci gaban da shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15 ke kawo da kuma budaddiyar fuskar Sin, wakilan CMG sun zanta da wasu shugabannin kamfanonin kasa da kasa dake da sassa a kasar Sin, bari mu ga ra’ayoyinsu game da hakan.

Shehun malami a cibiyar nazarin harkokin Asiya ta jami’ar kasar Singapore, Kishore Mahbubani ya bayyana cewa, kasar Sin ce kasa daya tilo a duniya da ta dauki matakin shirya bikin baje kolin kayayyakin da ake shigarwa kasarta, yana mai bayyana hakan a matsayin mai matukar ma’ana.

Shehun malamin ya kara da cewa, “A ganina, kasar Sin tana da idon basira, la’akari da yadda take aiwatar da shirye-shiryen raya kasa na shekaru biyar-biyar, matakin da ya sa kason kasar a duniya ta fannin sana’o’in kere-kere ya yi ta karuwa, adadin ake sa ran zai kai 45% ya zuwa 2030, maimakon yadda ya kasance a kaso 5% kawai a shekarar 2000.

ADVERTISEMENT

An baje kolin sabbin kayayyaki da fasahohi da ma hidimomi da yawansu ya kai har 461 a gun bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin na kasa da kasa karo na takwas da ke gudana a birnin Shanghai na kasar Sin (CIIE). Amma me ya sa kamfanoni masu jarin waje suke ta kokarin baje kolin sabbin kayayyakinsu a gun bikin?

Zhong Zhonglin, shugaban Nippon Paint reshen Sin ya ce, “Bayan an kammala wannan cikakken zama, mun ga manufofin Sin sun kara budewa ga ketare, kuma sun fi karbar jarin kasashen waje. Muna da kwarin gwiwa sosai game da kasuwar Sin.”

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Zhang Lei, mataimakiyar shugaban sashen yada labaru na kamfanin BaySystems reshen Sin da yankin arewa maso gabashin Asiya, ta kara da cewa, “A cikin shekaru 140 da suka gabata, mu kasance a nan ba mu taba barin ba, ko a lokacin wahala ko a’a. Wannan yana nuna irin kauna da alkawarin da wannan tsohon kamfanin Jamus mai shekaru 100 ke da su ga kasar Sin.”

A game da hakan, Frank Hammes, babban darektan kamfanin IQAir na kasar Switzerland ya bayyana cewa, bikin CIIE tamkar dakin gwaje-gwaje ne a gare mu, inda ban da baje kolin sabbin nasarorinmu, muna kuma iya samun martani daga masu sayayya.

Shi kuma Mr. Yu Feng, babban darektan kamfanin Honeywell da ke kula da harkokin kasar Sin, ya ce, masu sayayya wadanda da wuya a biya bukatunsu, alheri ne ga kamfanonin kirkire-kirkiren fasahohin zamani, sabo da su ne suke taimakawa wajen kirkiro sabbin fasahohin zamani.

“Za mu ci gaba da zuba jari a Sin har na karni 1”, “Za mu kara kusan shaguna 100 a Sin”. Nicolas Hieronimus shugaban kamfanin L’Oréal da Sandeep Seth, babban ma’aikacin kamfanin Tapestry sun fadi hakan yayin zantawar da wakilin CMG ya yi musu.

Hieronimus ya ce, “Sin ita ce kasuwa ta biyu mafi girma a duniya gare mu, kuma cibiyar kirkira ce mai karfi.” Seth kuma ya ce, “Kasuwar Sin ta zama filin gwajin sabbin dabaru.”

Wadannan kalamai sun nuna yadda suke amincewa da CIIE, tare da bayyana niyyar su ta ci gaba da fadada kasuwancinsu a Sin. (Lubabatu Lei da Amina Xu)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
  • Sulaiman
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
  • Sulaiman
    Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita
  • Sulaiman
    Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

MASU ALAKA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
Daga Birnin Sin

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
Daga Birnin Sin

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Next Post
An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.